Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Nahum 1:4 - Littafi Mai Tsarki

4 Yakan tsauta wa teku, sai teku ta ƙafe. Yakan busar da koguna duka. Bashan da Karmel sukan bushe, Tohon Lebanon yakan yanƙwane.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

4 Yakan tsawata wa teku yă kuma busar da shi; yakan sa dukan koguna su kafe. Bashan da Karmel sun yi yaushi tohon Lebanon kuma ya koɗe.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Nahum 1:4
22 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ƙasar na zaman banza, an gudu an bar ta. Jejin Lebanon ya bushe, kwarin Sharon mai dausayi ya zama kamar hamada, a Bashan kuma da a kan Dutsen Karmel sai ganyaye suke karkaɗewa daga itatuwa.


Ya tsauta wa Bahar Maliya, ta ƙafe, Har ya bi da jama'arsa su haye Kamar a bisa busasshiyar ƙasa.


Kai ne ka sa teku ta ƙafe, Ka kuma shirya hanya ta ruwa, Domin waɗanda kake cetonsu su haye.


Me ya faru ne, ya teku, da ya sa ki gudu? Kai fa Urdun, me ya sa ka daina gudu?


Bahar Maliya da ya duba, sai ya gudu, Kogin Urdun ya daina gudu.


Amma sa'ad da ka tsauta wa ruwa, Sai ya tsere, Sa'ad da ya ji ka daka tsawa, Sai ya sheƙa a guje.


Ka sa ruwan maɓuɓɓugai ya yi gudu, Ka sa manyan koguna su ƙafe.


Ya ce musu, “Don me kuka firgita haka, ya ku masu ƙarancin bangaskiya?” Sa'an nan ya tashi, ya tsawata wa iskar da ruwan. Sai wurin duk ya yi tsit!


Ubangiji ne ya yi taurarin Kaza da 'ya'yanta Da mai farauta da kare. Ya mai da duhu haske, Rana kuwa dare. Shi ya kirawo ruwan teku ya bayyana, Ya shimfiɗa shi a bisa ƙasa. Sunansa Ubangiji ne.


Amos ya ce, “Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona, Muryarsa za ta yi tsawa daga Urushalima. Da jin wannan, sai wuraren kiwo za su bushe, Ƙwanƙolin Dutsen Karmel, da yake kore zai yi yaushi.”


Zan busar da Kogin Nilu, Zan kuma sayar da ƙasar ga mugaye. Zan sa ƙasar ta lalace Da dukan abin da yake cikinta, Ta hannun baƙi, Ni Ubangiji, na faɗa.”


Na ce mata, ‘Iyakar inda za ki tsaya ke nan, Ba za ki wuce ba. Nan raƙuman ruwanki masu tumbatsa za su tsaya.’


Allah kuwa ya tuna da Nuhu da dukan dabbobin gida da na jeji waɗanda suke cikin jirgi tare da shi. Allah ya sa iska ta hura bisa duniya, ruwaye suka janye.


sai ruwan da yake gangarowa ya tsaya, ya tattaru wuri ɗaya, ya yi soro daga nesa kusa da Adam, birnin da yake kusa da Zaretan. Ruwan kuma da yake gangarowa zuwa Tekun Araba, wato Tekun Gishiri, aka yanke shi ɗungum. Jama'a kuwa suka haye daura da Yariko.


An bayyana ƙarƙashin teku a fili, An tone tussan duniya, Lokacin da Ubangiji ya yi wa abokan gāba tsautawa, Ya yi musu ruri cikin fushi.


Zan lalatar da tuddai da duwatsu, In kuma busar da ciyawa da itatuwa, Zan mai da kwaruruka inda akwai rafi hamada, In kuma busar da kududdufan ruwa.


Kifayen teku, da tsuntsayen sararin sama, da bisashe, da dukan masu rarrafe, da dukan mutanen da suke duniya, za su yi makyarkyata a gabana. Za a jefar da duwatsu ƙasa, tsaunuka za su fādi, kowane bango zai rushe.


Ubangiji ya miƙa hannunsa daga samaniya ya ɗauke ni, Ya tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ