Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




M.Sh 33:27 - Littafi Mai Tsarki

27 Allah Madawwami, shi ne wurin zamanka, Madawwaman damatsansa suna tallafarka, Yana kore maka maƙiyanka, Ya ce, ‘Ka hallaka su!’

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

27 Allah madawwami shi ne mafakarka, a ƙarƙashina kuma madawwamin hannuwa ne. Zai kore abokin gābanka a gabanka, yana cewa, ‘Ka hallaka shi!’

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




M.Sh 33:27
48 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ubangiji ne Mai Cetona, Shi ne garkuwata mai ƙarfi. Allahna, shi ne yake kiyaye ni, Lafiya nake sa'ad da nake tare da shi, Yana kiyaye ni kamar garkuwa, Yana kāre ni, ya ba ni lafiya.


Matalauta da 'yan ƙaƙa naka yi sun sheƙa zuwa wurinka, Sun sami zaman lafiya a lokatan wahala. Ka ba su mafaka daga hadura, Ka inuwantar da su daga matsanancin zafi. Mugaye sukan tasar musu kamar hadirin ƙanƙara,


Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, Kullum a shirye yake yă yi taimako a lokacin wahala.


Sunan Ubangiji kamar ƙaƙƙarfar hasumiya ne, inda adali yakan shiga ya zauna lafiya.


Allah mai ba da salama kuwa, zai sa ku tattake Shaiɗan da hanzari. Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu yă tabbata a gare ku.


Domin ka ɗauka Ubangiji yake kiyaye ka, Maɗaukaki ne yake tsaronka,


wato, ku da ikon Allah yake kiyayewa ta wurin bangaskiyarku, domin samun ceton nan da aka shirya a bayyana a ƙarshen zamani.


Ga wanda yake da iko yă tsare ku daga faɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa aibi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki,


Gama haka wanda yake can Sama, Maɗaukaki, wanda ake kira Mai Tsarki ya ce, “Ina zaune a can Sama a tsattsarkan wuri, tare kuma da wanda yake da halin tuba mai tawali'u, don in farfaɗo da ruhun masu tawali'u, in kuma farfaɗo da zukatan masu tuba.


Ko wannensu zai zama kamar wurin fakewa daga iska da kuma wurin ɓuya saboda hadiri, za su zama kamar rafuffukan da suke gudu cikin hamada, kamar inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.


Ku dogara ga Ubangiji har abada. Zai kiyaye mu kullayaumin.


Shi kuwa Ibilis mayaudarinsu, sai da aka jefa shi a tafkin wuta da ƙibiritu, a inda dabbar nan da annabin nan na ƙarya suke, za a kuma gwada musu azaba dare da rana har abada abadin.


Ya Allahna, kada ka ɗauke ni a yanzu, Tun da yake ban tsufa ba tukuna! Ya Ubangiji har abada kake.


Duk da haka bakunansu sun kakkarye. Damatsansu sun yayyage Ta wurin ikon Allah Mai Girma na Yakubu, Makiyayi, Dutse na Isra'ila.


Ga shi, an haifa mana ɗa! Mun sami yaro! Shi zai zama Mai Mulkinmu. Za a kira shi, “Mashawarci Mai Al'ajabi,” “Allah Maɗaukaki,” “Uba Madawwami,” “Sarkin Salama.”


balle fa jinin Almasihu wanda ya miƙa kansa marar aibu ga Allah, ta wurin Madawwamin Ruhu, lalle zai tsarkake lamirinmu daga barin ibada marar tasiri, domin mu bauta wa Allah Rayayye.


Girma da ɗaukaka su tabbata ga Sarkin zamanai, marar mutuwa, marar ganuwa, Allah Makaɗaici, har abada abadin. Amin, amin.


a kuma same ni a cikinsa, ba da wani adalcin kaina ba, wanda ya danganta da bin Shari'a, sai dai da adalcin nan wanda yake tsirowa daga bangaskiya ga Almasihu, wato, da adalcin nan wanda yake samuwa daga Allah ta wurin bangaskiya.


Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya, Shi Allah mai rai ne, Shi Sarki ne madawwami. Saboda hasalarsa duniya ta girgiza, Al'ummai ba za su iya jurewa da fushinsa ba.


Bari ka ta da kaina da hannun hagunka, Ka rungume ni da hannun damanka.


Sa'ad da suka kira gare ni, zan amsa musu, Zan kasance tare da su sa'ad da suke shan wahala, Zan cece su in girmama su.


Ka'idar nan ta Ruhu mai ba da rai da yake ga Almasihu Yesu ta 'yanta ni daga ka'idar zunubi da ta mutuwa.


“Ya mutanen Urushalima! Ya mutanen Urushalima! Masu kisan annabawa, masu jifan waɗanda aka aiko gare ku! Sau nawa ne ina so in tattaro ku kamar yadda kaza take tattara 'yan tsakinta a cikin fikafikanta, amma kun ƙi!


“Baitalami cikin Efrata, Wadda kike 'yar ƙarama a cikin kabilar Yahuza, Amma daga cikinki wani zai fito wanda zai sarauci Isra'ila Wanda asalinsa tun fil azal ne.”


Hadiri yakan taso ya wargaza mugaye, amma amintattu lafiya lau suke a ko yaushe.


Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu, Allah na Yakubu shi ne mafakarmu!


Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu, Allah na Yakubu shi ne mafakarmu!


Ina misalin darajar madawwamiyar ƙaunarka, ya Ubangiji! Mutane sukan sami mafaka a ƙarƙashin fikafikanka.


A lokatan wahala zai kiyaye ni a inuwarsa, Zai kiyaye ni lafiya a Haikalinsa, Zai ɗora ni a kan dutse mai tsayi, ya kiyaye ni.


Gama Maɗaukaki na Isra'ila ba zai yi ƙarya, ko ya sāke nufinsa ba. Shi ba mutum ba ne, da zai sāke nufinsa.”


Sa'ad da Ubangiji Allahnku ya bashe su a hannunku, kuka kuma ci nasara a kansu, sai ku hallaka su sarai. Kada ku yi alkawari da su, kada kuma ku yi musu jinƙai.


Allah ya nuna akwai zaman lafiya a wurinsa, A kagarar birnin.


Ubangiji kuwa ya kore mana dukan Amoriyawa waɗanda suke zaune a ƙasar, domin haka za mu bauta wa Ubangiji, gama shi ne Allahnmu.”


Ku kiyaye abin da na umarce ku a wannan rana. Ga shi, zan kora muku Amoriyawa, da Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa.


Allah, shi wanda yake mulki tun fil azal, Zai ji ni, zai kore su. Ba abin da suka iya yi a kai, Domin ba su tsoron Allah.


Ka zama mini lafiyayyiyar mafaka, Da kagara mai ƙarfi, domin ka tsare ni, Kai ne mafakata da kāriyata.


Ba kai ne madawwami ba? Ya Ubangiji Allahna Mai Tsarki. Ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji, kai ne ka sa su su yi hukunci, Ya dutse, kai ne ka kafa su don su yi horo.


Zan aiki zirnako a gabanku, su kore muku Hiwiyawa, da Kan'aniyawa, da Hittiyawa.


Ku yi shelar ikon Allah, Ɗaukakarsa tana bisa kan Isra'ila, Ikonsa yana cikin sararin sama.


Kana kewaye da ni a kowane sashe, Ka kiyaye ni da ikonka.


“Ku haura ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da mazaunan Fekod. Ku kashe, ku hallaka su sarai, Ku aikata dukan abin da na umarce ku, Ni Ubangiji na faɗa.


Ko da yake ni ne na koya wa Ifraimu tafiya. Na ɗauke su a hannuna, Amma ba su sani ni ne na lura da su ba.


Ki tattara sojojinki, gama an kewaye mu da yaƙi. Za su bugi kumatun Sarkin Isra'ila da sanda.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ