Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




M.Sh 33:12 - Littafi Mai Tsarki

12 A kan Biliyaminu, ya ce, “Shi ƙaunatacce na Ubangiji ne, Yana zaune lafiya kusa da shi, Ubangiji yana yi masa garkuwa dukan yini, Yana zaune a kan kafaɗunsa.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

12 Game da Benyamin ya ce, “Bari ƙaunataccen Ubangiji yă zauna lafiya kusa da shi, gama yana tsare shi dukan yini, wanda kuma Ubangiji yake ƙauna yana zama a tsakanin kafaɗunsa.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




M.Sh 33:12
24 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

sai ya fita ya taryi Asa, ya ce masa, “Ka ji ni, ya Asa, kai da dukan Yahuza da Biliyaminu, Ubangiji yana tare da ku idan kuna tare da shi. Idan kuwa kun neme shi, za ku same shi, amma idan kun rabu da shi, shi ma zai rabu da ku.


“Ya mutanen Urushalima! Ya mutanen Urushalima! Masu kisan annabawa, masu jifan waɗanda aka aiko a gare ku! Sau nawa ne na so in tattaro ku kamar yadda kaza take tattara 'yan tsakinta cikin fikafikanta, amma kun ƙi!


Zai rufe ka da fikafikansa, Za ka zauna lafiya a ƙarƙashinsu. Amincinsa zai tsare ka, ya kiyaye ka.


Na shimfiɗa sammai, Na kafa harsashin ginin duniya, Na ce wa Sihiyona, ‘Ku jama'ata ne! Na ba ku koyarwata, Na kuwa kiyaye ku da ikona.’ ”


Zan kāre wannan birni in kiyaye shi, saboda girmana, domin kuma alkawarin da na yi wa bawana Dawuda.’ ”


Ubangiji ya ce, “Birnin Urushalima yana yi maka dariya, kai Sennakerib, yana kuma yi maka ba'a.


Sa'ad da Rehobowam ya kai Urushalima, sai ya tattara zaɓaɓɓun mayaƙa, mutum dubu ɗari da dubu tamanin (180,000) daga cikin jama'ar Yahuza da ta Biliyaminu don su yi yaƙi da Isra'ila, su komo wa Rehobowam da mulki.


Da Rehobowam ya komo Urushalima, sai ya tara dukan jama'ar gidan Yahuza, da na kabilar Biliyaminu. Aka sami mayaƙa dubu ɗari da dubu tamanin (180,000) waɗanda za su yi yaƙi da gidan Isra'ila, don su komar da su a ƙarƙashin mulkin Rehobowam, ɗan Sulemanu.


Amma sa'ad da kuka haye Urdun, kuka zauna a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ita gādo, sa'ad da kuma ya ba ku hutawa daga maƙiyanku waɗanda suke kewaye da ku, kuka sami zaman lafiya,


“A nan zan zauna har abada. A nan kuma nake so in yi mulki.


Amma mutanen Biliyaminu ba su kori Yebusiyawan da suke zaune a Urushalima ba domin haka Yebusiyawa suka yi zamansu tare da mutanen Biliyaminu a Urushalima har wa yau.


A sa duwatsun a kafaɗun falmaran domin a riƙa tunawa da 'ya'yan Isra'ila. Haruna zai rataya sunayensu a kafaɗunsa a gaban Ubangiji domin a tuna da su.


Elidad ɗan Kislon daga kabilar Biliyaminu.


Saboda ya ƙaunaci kakanninku shi ya sa ya zaɓi zuriyarsu a bayansu, shi kansa kuma ya fisshe ku daga Masar da ikonsa mai girma.


Kamar gaggafar da take kaɗa fikafikanta a kan sheƙarta, Tana rufe da 'yan tsakinta, Ta buɗe fikafikanta, ta kama su, Ta ɗauke su a bisa kafaɗunta.


Ya Ubangiji ka inganta jaruntakarsu, Ka karɓi aikin hannuwansu, Ka murƙushe ƙarfin abokan gābansu, Da waɗanda suke ƙinsu don kada su ƙara tashi.”


Ka cece mu da ƙarfinka, ka amsa addu'ata, Domin jama'ar da kake ƙauna ta sami cetonka.


Sa'an nan Sama'ila ya ce wa kabilan Isra'ila su guso, kuri'a kuwa ta faɗa a kan kabilar Biliyaminu.


Sa'an nan Dawuda ya yi wa Batsheba, matarsa, ta'aziyya. Ya shiga wurinta, ya kwana da ita. Ta haifa masa ɗa. Ya raɗa masa suna Sulemanu. Ubangiji kuwa ya ƙaunace shi,


ya kuma umarci annabi Natan ya raɗa wa yaron suna Yedideya, wato ƙaunataccen Ubangiji.


Ubangiji ya ce, “Na bar jama'ata. Na rabu da gādona, Na ba da wanda raina yake ƙauna a hannun maƙiyansa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ