Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




M.Sh 32:7 - Littafi Mai Tsarki

7 “Ku fa tuna da kwanakin dā, Ku yi tunani a kan shekarun tsararraki, Ku tambayi mahaifanku, su za su faɗa muku, Ku tambayi dattawanku, su kuma za su faɗa muku,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

7 Ku tuna da kwanakin dā, ku tuna da tsararrakin da suka wuce tun tuni, Ku tambayi iyayenku, za su faɗa muku, dattawanku, za su kuma bayyana muku.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




M.Sh 32:7
17 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Da kunnuwanmu muka ji, ya Allah, Kakanninmu suka faɗa mana, Manya manyan abubuwa da ka aikata a lokacinsu, A zamanin dā,


Ku tuna da abin da ya faru tuntuni, Ku sani, ni kaɗai ne Allah, Ba kuwa wani mai kama da ni.


“Ku tambaya mana, ko a kwanakin dā kafin zamaninku, tun ma daga lokacin da Allah ya yi mutum a duniya, ku tantambaya daga wannan kusurwa ta samaniya zuwa waccan, ko wani babban abu irin wannan ya taɓa faruwa, ko kuma an taɓa jin labarin irinsa?


Amma suka tuna da zamanin dā, zamanin Musa bawan Ubangiji, suka yi tambaya suka ce, “Yanzu fa, ina Ubangiji yake wanda ya ceci shugabannin jama'arsa daga teku? Ina Ubangiji yake, wanda ya ba Musa iko musamman?


In wata rana 'ya'yanku suka tambaye ku cewa, ‘Ina ma'anar wannan?’ Sai ku ce musu, ‘Da iko Ubangiji ya fisshe mu daga Masar, daga gidan bauta.


Sai Gidiyon ya ce masa, “Ya shugabana, idan Ubangiji yana tare da mu, me ya sa abubuwan nan suka same mu? Ina kuma ayyukansa masu ban al'ajabi waɗanda kakanninmu suka faɗa mana cewa, ‘Ai, Ubangiji ne ya fisshe mu daga Masar’? Amma yanzu Ubangiji ya yi watsi da mu, ya ba da mu ga Madayanawa.”


Na tuna da koyarwar da ka yi mini a dā, Sukan kuwa ta'azantar da ni, ya Ubangiji.


Ya daina ƙaunata ke nan? Alkawarinsa ba shi da wani amfani?


Yana ce wa kansa “Ba zan taɓa fāɗuwa ba, Ba zan taɓa shan wahala ba.”


Sa'ad da 'ya'yanku suka tambaye ku, ‘Ina ma'anar wannan farilla?’


Ya ba da dokoki ga jama'ar Isra'ila, Da umarnai ga zuriyar Yakubu. Ya ba kakanninmu ka'idodi, Don su koya wa 'ya'yansu dokokinsa,


Ku tuna yadda Ubangiji Allahnku ya bishe ku shekarun nan arba'in a jeji don ya koya muku tawali'u. Ya jarraba ku don ya san zuciyarku, ko za ku kiyaye umarnansa ko babu.


Yadda kai da kanka ka kori arna, Ka dasa jama'arka a ƙasarsu, Yadda ka hori sauran al'umma, Amma ka sa jama'arka su wadata.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ