Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




M.Sh 32:29 - Littafi Mai Tsarki

29 Da suna da hikima, da sun gane wannan, Da za su gane da yadda ƙarshensu zai zama!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

29 A ce su masu hikima ne har su gane wannan su gane abin da ƙarshensu zai zama!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




M.Sh 32:29
18 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ina kuwa so jama'ata su kasa kunne gare ni, Su kuwa yi mini biyayya!


Da ma kullum suna da irin wannan zuciya ta tsorona, da za su kiyaye dukan umarnaina, zai zama fa'ida gare su da 'ya'yansu har abada.


Amma Allah ya ce masa, ‘Kai marar azanci! A daren nan za a karɓi ranka. To, kayan da ka tanada, na wa za su zama?’


Duk wanda yake da hikima, bari ya fahimci abubuwan nan. Duk wanda yake da ganewa, bari ya san abubuwan nan, Gama hanyoyin Ubangiji masu gaskiya ne, Masu adalci kuwa za su yi tafiya a cikinsu, Amma masu zunubi za su yi tuntuɓe a kansu.


Da ma a ce masu hikima Za su yi tunani a kan waɗannan abubuwa, Da ma kuma su yarda Da madawwamiyar ƙaunar Ubangiji.


Kina tsammani za ki yi ta zama sarauniya kullayaumin, Ba ki ɗauki waɗannan al'amura a zuci ba, Ko ki yi tunanin yadda za su ƙare.


Me za ku yi sa'ad Allah zai hukunta ku? Me za ku yi kuma sa'ad da ya kawo muku masifa daga wata ƙasa mai nisa? Ina za ku sheƙa neman taimako? A ina kuma za ku ɓoye dukiyarku?


Ƙazantarta tana cikin tufafinta, Ba ta tuna da ƙarshenta ba, Domin haka faɗuwarta abar tsoro ce, Ba ta da mai yi mata ta'aziyya. “Ya Ubangiji, ka dubi wahalata, Gama maƙiyi ya ɗaukaka kansa!”


“Kamar makwarwar da ta kwanta kan ƙwan da ba ita ta nasa ba, Haka yake ga wanda ya sami dukiyar haram, Yana gaɓar ƙarfinsa, za ta rabu da shi, A ƙarshe zai zama wawa.”


Annabawa sun yi annabcin ƙarya, Firistoci kuma sun yi mulki da ikon kansu, Mutanena kuwa suna so haka! Amma sa'ad da ƙarshe ya zo, me za ku yi?”


Dole su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa, Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu.


Gama na sani bayan rasuwata za ku aikata mugunta, ku kauce daga hanyar da na umarce ku. Masifa za ta auko muku a kwanaki masu zuwa saboda za ku aikata mugunta a gaban Ubangiji, za ku tsokani fushinsa da aikin hannuwanku.”


Ka koya mana mu sani ranmu na ɗan lokaci ne, Domin mu zama masu hikima.


Yanzu ku tuna a ran nan, wato rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, tun daga ranar da aka aza harsashin ginin Haikalin Ubangiji.


Ko akwai wanda zai kasa kunne ga wannan? Ko za ku kasa kunne ku yi lura daga yanzu?


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ