Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




M.Sh 32:19 - Littafi Mai Tsarki

19 “Ubangiji ya gani, ya raina su, Saboda tsokanar da 'ya'yansa mata da maza suka yi masa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

19 Ubangiji ya ga wannan ya kuma ƙi su, domin ’ya’yansa maza da mata sun husata shi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




M.Sh 32:19
18 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da jama'arsa, Ransa bai ji daɗinsu ba.


Ubangiji ya ce, “Duniya da sararin sama, ku kasa kunne ga abin da ni, Ubangiji, nake cewa! 'Ya'yan da na goya sun tayar mini.


Kai ba Allah mai yarda da aikin kuskure ba ne, Ba ka yarda da mugunta a gabanka.


Ubangiji kuwa ya husata da Isra'ilawa, ya bashe su ga waɗanda za su washe su. Ya sa magabtansu da suke kewaye da su suka sha ƙarfinsu, har ya zama Isra'ilawa ba su iya kāre kansu daga maƙiyansu ba.


To, saboda kai tsakatsaki ne, ba ka da sanyi, ba ka kuwa da zafi, zan tofar da kai daga bakina.


A wata guda na hallaka makiyayan nan uku, gama ban jure da su ba, su ma sun gaji da ni.


Ya rushe Haikalinsa kamar bukka cikin gona, Ya mai da wurin yin ƙayyadaddun idodinsa kufai. Ubangiji ya sa ƙayyadadden idi da kiyaye Asabar Su ƙare a Sihiyona, Da zafin fushinsa kuma ya wofinta sarki da firist.


Ubangiji ya ce, “Wane iko ƙaunatacciyata take da shi cikin Haikalina, da ya ke ta aikata mugayen ayyuka? Ko alkawarai da naman hadayu za su iya kawar miki da ƙaddararki, har da za ki yi taƙama?


Allah ya yi fushi sa'ad da ya ga haka, Don haka ya rabu da jama'arsa ɗungum.


Mugun mutum yana fāriya da mugayen manufofinsa, Mai haɗama yakan zagi Ubangiji ya kuma ƙi shi.


Zan kafa wurin zamana a tsakiyarku, ba kuwa zan gaji da ku ba.


Zan lalatar da masujadanku, in rurrushe bagaden ƙona turarenku, in jefar da gawawwakinku a kan gumakanku, raina kuwa zai ji ƙyamarku.


Amma kana fushi da zaɓaɓɓen sarkinka, Ka rabu da shi, ka yashe shi.


Shugaban matsara ya ware Irmiya, sa'an nan ya ce masa, “Ubangiji Allahnka ne ya hurta wannan masifa a kan wurin nan.


Ubangiji kansa ne ya rantse. Ubangiji Allah Mai Runduna ya ce, “Ba na son girmankai na jama'ar Isra'ila. Ba na son fādodinsu. Zan ba da birnin da dukan abin da yake cikinsa ga abokan gābansu.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ