Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




M.Sh 26:15 - Littafi Mai Tsarki

15 Ka duba ƙasa daga Sama, daga wurin zamanka mai tsarki, ka sa wa jama'arka, Isra'ila, albarka duk da ƙasar da ka ba mu, ƙasar da take mai yalwar abinci, kamar yadda ka rantse wa kakanninmu.’ ”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

15 Ka duba ƙasa daga sama, mazauninka mai tsarki, ka albarkace mutanenka Isra’ila da kuma ƙasar da ka ba mu kamar yadda ka yi wa kakanninmu alkawari da rantsuwa, ƙasa mai zub da madara da zuma.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




M.Sh 26:15
26 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ya Ubangiji, ka dube mu daga Sama, wurin da kake cike da tsarki da ɗaukaka. Ina kulawan nan da kake yi mana? Ina ikon nan naka? Ina ƙaunan nan taka da juyayin nan naka? Kada ka watsar da mu.


Bari dukan 'yan adam su yi tsit a gaban Ubangiji, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.


“ ‘Allah ya ce, Sama ita ce kursiyina, Ƙasa kuwa matashin ƙafata. Wane wuri kuma za ku gina mini? Ko kuwa wane wuri ne wurin hutuna?


Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya ce, “Nan gaba za su sāke yin magana a ƙasar Yahuza da biranenta a sa'ad da na mayar musu da dukiyarsu. “ ‘Ubangiji ya sa maka albarka, Ya wurin zaman adalci, Ya tsattsarkan tudu!’


sai ka kasa kunne ga addu'arsa. Ka ji daga Sama, wurin zamanka, ka amsa masa abin da ya roƙe ka, domin dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma yi tsoronka kamar jama'arka, Isra'ilawa, domin kuma su sani wannan Haikali da na gina wurin da za a yi maka sujada ne.


“Amma ko Allah zai zauna a duniya? Ga shi, Saman sammai ba ta isa ta karɓe ka ba, balle wannan Haikali da na gina!


Saboda haka sai ku yi addu'a kamar haka, “ ‘Ya Ubanmu, wanda yake cikin Sama, A kiyaye sunanka da tsarki.


Ubangiji ya saukar mini da ikonsa. Ya zaɓe ni, ya aike ni Domin in kawo albishir mai daɗi ga talakawa, In warkar da waɗanda suka karai a zuci, In yi shelar kwance ɗaurarru, Da kuma 'yanci ga waɗanda suke cikin kurkuku.


Gama haka wanda yake can Sama, Maɗaukaki, wanda ake kira Mai Tsarki ya ce, “Ina zaune a can Sama a tsattsarkan wuri, tare kuma da wanda yake da halin tuba mai tawali'u, don in farfaɗo da ruhun masu tawali'u, in kuma farfaɗo da zukatan masu tuba.


Ka yarda, albarkarka ta kasance tare da mu, ya Ubangiji Allahnmu. Ka sa mu yi nasara game da dukan abin da za mu yi! I, ka ba mu nasara a dukan abin da muke yi!


Ya Allah, ka yi wa Sihiyona alheri, ka taimake ta, Ka sāke gina garun Urushalima.


Ka ceci jama'arka, ya Ubangiji, Ka sa wa waɗanda suke naka albarka! Ka zama makiyayinsu, Ka lura da su har abada.


Amma muka yi kuka ga Ubangiji Allah na kakanninmu. Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya ga azabarmu, da wahalarmu, da zaluncin da ake yi mana.


Ubangiji ya kawo mu nan, ya ba mu ƙasar nan, ƙasar da take mai yalwar abinci.


Ban ci kome daga cikin zakar sa'ad da nake baƙin ciki ba, ban kuma fitar da kome daga cikinta ba sa'ad da nake da ƙazanta, ban kuma miƙa wa matattu kome daga cikinta ba. Na yi biyayya da muryar Ubangiji Allahna, na aikata dukan abin da ka umarce ni.


Sai firistoci da Lawiyawa suka tashi suka sa wa jama'a albarka, aka kuwa ji muryarsu, addu'arsu kuma ta kai wurin zamansa a Sama.


Allah, wanda yake zaune a tsattsarkan Haikalinsa, Yana lura da marayu, yana kuwa kiyaye gwauraye, Wato matan da mazansu suka mutu.


Ka juyo wurinmu, ya Allah Mai Runduna! Daga Sama, ka dube mu, Ka zo ka ceci kurangar inabinka!


Duba, na sa ƙasar a gabanku, sai ku shiga ku mallake ta, ƙasa wadda na rantse wa kakanninku, wato Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, cewa zan ba su, su da zuriyarsu a bayansu.’ ”


Don haka, ku ji, ya Isra'ilawa, ku lura, ku kiyaye su domin zaman lafiyarku, domin kuma ku riɓaɓɓanya ƙwarai a ƙasar da take mai yalwar abinci yadda Ubangiji Allah na kakanninku ya alkawarta muku.


Ka zo ka ceci kurangar inabin nan Wadda kai da kanka ka dasa, Wannan ƙaramar kuranga, Ka sa ta yi girma, ta yi ƙarfi sosai!


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ