Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Mika 7:8 - Littafi Mai Tsarki

8 Ya maƙiyina, kada ka yi murna a kaina, Gama sa'ad da na fāɗi, zan tashi kuma. Sa'ad da na zauna cikin duhu, Ubangiji zai haskaka ni.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Kada ku yi farin ciki, ku maƙiyana! Ko da yake na fāɗi, zan tashi. Ko da yake na zauna a cikin duhu, Ubangiji zai zama haskena.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Mika 7:8
46 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Sai Yesu ya ƙara musu da cewa, “Ni ne Hasken duniya. Wanda yake bi na ba zai yi tafiya a duhu ba, amma zai sami hasken rai,”


Jama'ar da suka yi tafiya cikin duhu, Sun ga babban haske! Suka zauna a inuwar mutuwa, Amma yanzu haske ya haskaka su.


Haske yakan haskaka wa mutanen kirki a cikin duhu, Da waɗanda suke yin alheri, da jinƙai, da gaskiya.


Ubangiji ne haskena da cetona, Ba zan ji tsoron kowa ba. Ubangiji yana kiyaye ni daga dukan hatsari, Ba zan ji tsoro ba.


Ba daidai ba ne ka yi murna Saboda wahalar da ta sami ɗan'uwanka. Ba daidai ba ne ka yi farin ciki Saboda halakar mutanen Yahuza. Ba daidai ba ne ka yi musu dariya A ranar wahalarsu.


Domin shi Allah wanda ya ce, “Haske yă ɓullo daga duhu ya haskaka,” shi ne ya haskaka zukatanmu domin a haskaka mutane su san ɗaukakarsa a fuskar Yesu Almasihu.


Kada ka bar magabtana su yi murna saboda wahalata. Kada ka bar su su yi kirari a kan faɗuwata!


Ba za a ƙara yin dare ba, ba za su bukaci hasken fitila, ko na rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su, za su kuma sha ni'imar Mulki har abada abadin.


Ubangiji shi ne makiyayinmu, sarkinmu mai daraja, Yakan sa mana albarka, da alheri, da daraja, Ba ya hana kowane abu mai kyau ga waɗanda suke aikata abin da yake daidai.


“Idan na yi murna saboda wahala ta sami maƙiyana, Ko na yi fariya saboda mugun abu ya same shi,


Haske yakan haskaka adalai, Haka kuma murna ta cika ga masu nagarta.


Kamar yadda ya yi farin ciki saboda gādon jama'ar Isra'ila, da ya zama kufai marar amfani, haka nan zan yi da shi, wato Seyir. Zai zama kufai marar amfani, wato Dutsen Seyir da dukan Edom. Sa'an nan mutane za su sani ni ne Ubangiji!”


Kada ka bar maƙiyana, maƙaryatan nan, su ga fāɗuwata! Kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, Su ƙyaface ni, su yi murna saboda baƙin cikina!


Lalle hakika, ina gaya muku, za ku yi kuka da kuma gunji, amma duniya za ta yi farin ciki. Za ku yi baƙin ciki, amma baƙin cikinku zai koma farin ciki.


Amma ku da kuke yi mini biyayya, ikon cetona zai fito muku kamar rana. Zai kawo warkarwa kamar hasken rana. Za ku fita kuna tsalle kamar 'yan maruƙan da aka fisshe su daga garke.


Sa'an nan maƙiyina wanda suke ce mini, “Ina Ubangiji Allahnka?” Zai gani, ya kuma ji kunya. Idanuna za su gan shi lokacin da aka tattake shi Kamar taɓo a titi.


Gama Ubangiji Allah ya ce, “Da yake kun tafa hannuwanku, kun buga ƙafafunku, kuka yi murna don nuna dukan ƙiyayyarku da ƙasar Isra'ila,


domin ka buɗe musu ido, su juyo daga duhu zuwa haske, daga kuma mulkin Shaiɗan zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai, da kuma gādo tare da dukan tsarkaka saboda sun gaskata da ni.’ ”


“Wata rana zan sāke tayar da birnin Dawuda Tankar yadda akan ta da gidan da ya rushe. Zan gyara garunsa, in sāke mai da shi. Zan sāke gina shi in mai da shi kamar yadda yake tun dā.


Mazaunan duhu sun ga babban haske, Mazaunan bakin mutuwa da fargabarta, Haske ya keto musu.”


“Saboda kuna murna, kuna farin ciki, Ku da kuka washe gādona, Saboda kuma kuna tsalle kamar karsana a cikin ciyawa, Kuna haniniya kamar ingarmu,


Zan ce wa 'yan kurkuku, ‘Ku tafi na sake ku!’ Waɗanda suke cikin duhu kuwa, in ce musu, ‘Ku fito zuwa wurin haske!’ Za su zama kamar tumakin da suke kiwo a tuddai,


Yanzu fa, zuriyar Yakubu, bari mu yi tafiya a cikin hasken da Ubangiji ya ba mu!


In ya fāɗi, ba zai yi warwar ba, Gama Ubangiji zai taimake shi Yă tashi tsaye.


Mugu yakan ci bashi, yă ƙi biya, Amma mutumin kirki mai alheri ne, Mai bayarwa hannu sake.


Birnin kuwa ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi, domin ɗaukakar Allah ita ce haskensa, Ɗan Ragon kuma fitilarsa.


Ku duka da kuke tsoron Ubangiji, Kuna kuma biyayya da kalmomin bawansa, Zai yiwu hanyar da kuke bi ta yi duhu ƙwarai, Amma ku dogara ga Ubangiji, ku jingina ga Allahnku.


Ana tsananta mana, duk da haka ba mu zama yasassu ba. Ana ta fyaɗa mu a ƙasa, duk da haka ba a hallaka mu ba.


Za su yi tuntuɓe su fāɗi, Amma mu za mu tashi mu tsaya daram!


“Ka faɗa musu, ka ce, ni Ubangiji na ce, ‘Wanda ya fāɗi ba zai sāke tashi ba? Idan wani ya kauce ba zai komo kan hanya ba?


Kin yi wa mutanen Isra'ila dariya. A kowane lokacin da kika ambaci sunansu, sai ki taɗa kanki da raini kamar an kama su tare da ɓarayi.


ni, Ubangiji Allah, ina yin magana da zafin kishina gāba da sauran al'umma, da dukan Edom, gama da farin ciki da raini suka mallaki ƙasata, suka washe ta.’


Ki yi makyarkyata, ki yi nishi, ke Sihiyona, Kamar mace mai naƙuda, Gama yanzu za ki fita daga cikin birni, Ki zauna a karkara, Za ki tafi Babila, daga can za a cece ki. Daga can Ubangiji zai cece ki daga hannun maƙiyanki.


A ranar, Ubangiji zai kiyaye mazaunan Urushalima, har wanda yake marar ƙarfi a cikinsu zai zama mai ƙarfi kamar Dawuda. Jama'ar Dawuda za ta zama kamar Allah, kamar mala'ikan Ubangiji a gabansu.


Maƙiyina ya tsananta mini, Ya kore ni fata-fata. Ya sa ni a kurkuku mai duhu, Ina kama da waɗanda suka daɗe da mutuwa,


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ