Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Mika 6:2 - Littafi Mai Tsarki

2 “Ku duwatsu da madawwaman tussan duniya, Ku ji tuhumar da Ubangiji yake yi muku. Gama Ubangiji, yana da magana gāba da mutanensa, Zai tuhumi Isra'ila.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

2 “Ku saurara, ya ku duwatsu game da tuhumar da Ubangiji yake muku, ku ji, ku daɗaɗɗun tushin duniya. Gama Ubangiji yana da ƙara a kan mutanensa; yana tuhumar Isra’ila.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Mika 6:2
19 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ubangiji yana da magana game da mutanen Yahuza, Zai hukunta Isra'ila saboda hanyoyinta, Zai sāka mata gwargwadon ayyukanta.


Ya ku mutanen Isra'ila, ku ji maganar Ubangiji, Gama Ubangiji yana da shari'a da ku, ku mazaunan ƙasar. “Gama ba gaskiya, ko ƙauna, Ko sanin Ubangiji a ƙasar.


Ubangiji ya ce, “Yanzu fa, bari mu daidaita al'amarinmu. Duk kun yi ja wur da zunubi, amma zan wanke ku, ku yi fari fat kamar auduga. Zai yiwu zunubinku ya sa ku zama ja wur, amma za ku yi fari fat kamar farin ulu.


Ka sa duniya ta kahu sosai a bisa harsashin gininta, Ba kuwa za a iya kawar da ita ba har abada.


An bayyana ƙarƙashin teku a fili, An tone tussan duniya, Lokacin da Ubangiji ya yi wa abokan gāba tsautawa, Ya yi musu ruri cikin fushi.


Gama fushina ya kama wuta, Tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za ta cinye duniya da dukan amfaninta, Za ta kama tussan duwatsu.


Idan a iya auna sammai a kuma iya bincike tushen duniya a ƙarƙas, To, ashe, zan watsar da dukan zuriyar Isra'ila ke nan saboda dukan abin da suka yi, Ni Ubangiji na faɗa.


Za a ji hayaniya har iyakar duniya, Gama Ubangiji yana da ƙara game da al'ummai, Zai shiga hukunta wa dukan 'yan adam, Zai kashe mugaye da takobi, Ubangiji ya faɗa.’ ”


“Domin haka, ni Ubangiji zan gabatar da ku gaban shari'a. Ku da 'ya'yanku, da 'ya'yan 'ya'yanku, wato jikokinku.


“Bari mu tafi ɗakin shari'a, ku kawo ƙararrakinku. Ku gabatar da matsalarku don a tabbatar kuna da gaskiya!


Saboda haka, abokina ya ce, “Ku jama'ar da yake zaune a Urushalima da Yahuza, ku shara'anta tsakanina da gonar inabina.


Ya kuma umarci ruwan teku, kada ya zarce wurin da ya sa. Ina can sa'ad da ya kafa harsashin ginin duniya.


“Sa'an nan duniya ta yi tangaɗi, ta girgiza, Harsashin sararin sama ya yi makyarkyata, ya raurawa, saboda fushin Allah.


to, yau na kira sama da duniya su shaida a kanku, cewa lalle za ku hallaka nan da nan cikin ƙasar da za ku haye Urdun zuwa cikinta don ku mallake ta. Ba za ku daɗe cikinta ba, amma za a shafe ku ƙaƙaf.


Ubangiji a shirye yake ya hurta maganarsa, a shirye yake ya hukunta al'ummai.


“Ku ji abin da ni Ubangiji nake cewa, Tashi ku gabatar da ƙararku a gaban duwatsu, Ku bar tuddai su ji muryarku.


A cikin mahaifa kakansu Yakubu ya kama diddigen ɗan'uwansa, Sa'ad da ya zama baligi ya yi kokawa da Allah.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ