Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Makoki 5:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Ya Ubangiji, ka tuna da abin da ya same mu. Ka duba, ka ga yadda muka zama abin kunya!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Makoki 5:1
26 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ya Ubangiji, na ji labarinka, Sai tsoro ya kama ni. Ka maimaita manyan ayyukanka a zamaninmu, Ayyukan da ka saba yi. Ka yi jinƙai ko lokacin da kake fushi.


“Ya Ubangiji, ka ji zargi Da dukan dabarun da suke yi mini.


Ka tuna da azabata, da galabaitata, Da ɗacin raina, da kumallon da nake fama da shi.


Dukan masu wucewa suna yin miki tafin raini. Suna yi wa Urushalima tsāki, Suna kaɗa mata kai, suna cewa, “Ai, Urushalima ke nan, Birnin nan da ake cewa mai cikakken jamali, Wanda ya ƙayatar da dukan duniya?”


Sa'an nan Irmiya ya ce, “Ya Ubangiji, ka sani. Kai ne, ka ziyarce ni, Ka kuma sāka wa waɗanda suke tsananta mini. Ka sani saboda kai nake shan zargi.


Ya Ubangiji, ka rama wa al'umman nan har sau bakwai, Saboda tsiwace-tsiwacen da suka yi maka.


Sauran al'ummar da take kewaye da mu, Suka maishe mu abin ba'a, suka yi mana dariya, Suka yi mana ba'a.


Sai ni, Nehemiya, na yi addu'a, na ce, “Ka ji, ya Allahnmu, gama ana raina mu, ka sa ba'arsu ta koma kansu, ka sa a washe su a kai su ƙasar bauta.


Ya kuma ce, “Ya Yesu, ka tuna da ni, sa'ad da ka shiga sarautarka.”


Ya Ubangiji, ka duba, ka gani! Wane ne ka yi wa haka? Mata za su cinye 'ya'yansu da suke reno? Ko kuwa za a kashe firist da annabi A cikin Haikalin Ubangiji?


“Ka duba, ya Ubangiji, ina shan wahala, Raina yana cikin damuwa, Zuciyata tana makyarkyata saboda tayarwata. A titi takobi yana karkashewa, A gida kuma ga mutuwa.


Ka tuna, ya Allah, kai ka halicce ni, da yumɓu kuwa ka yi ni. Za ka murtsuke ni ne, in kuma koma ƙura?


“Ka tuna, ya Ubangiji, raina iska ne kawai, Farin cikina ya riga ya ƙare.


Ka tuna da maganar da ka umarci bawanka Musa cewa, ‘Idan kun yi rashin aminci, zan warwatsa ku cikin al'ummai.


Sai suka ce mini, “Waɗanda suka tsira, suka koma daga zaman talala, da suke can lardin, suna cikin wahala ƙwarai, suna kuma shan kunya. Garun Urushalima kuma ya rushe, ƙofofi sun ƙone.”


Ka dubi wahalata, ka cece ni, Gama ban ƙi kulawa da dokarka ba.


Ya Urushalima, na sa matsara a garukanki Ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Za su tuna wa Ubangiji da alkawaransa, Ba kuwa za su bari ya manta ba!


Har lokacin da Ubangiji daga Sama ya duba, ya gani.


Amma ka tuna fa, ya Ubangiji, abokan gābanka suna yi maka ba'a, Su wawaye ne waɗanda suke raina ka.


Mun sha kunya saboda zargin da ake yi mana, Kunya ta rufe mu, Gama baƙi sun shiga tsarkakan wurare na Haikalin Ubangiji.


Ƙazantarta tana cikin tufafinta, Ba ta tuna da ƙarshenta ba, Domin haka faɗuwarta abar tsoro ce, Ba ta da mai yi mata ta'aziyya. “Ya Ubangiji, ka dubi wahalata, Gama maƙiyi ya ɗaukaka kansa!”


Dukan jama'arta suna nishi don neman abinci, Sun ba da kayansu masu daraja saboda abinci Don su rayu. “Ya Ubangiji ka duba, ka gani, Gama an raina ni.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ