Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Makoki 3:24 - Littafi Mai Tsarki

24 Na ce, “Ubangiji shi ne nawa, Saboda haka zan sa zuciya gare shi.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Makoki 3:24
25 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Kwanyata da jikina za su raunana, Amma Allah ne ƙarfina, Shi nake so har abada!


Kai ne kaɗai, nake da shi, ya Ubangiji, Kai ne kake biyan dukan bukatata, Raina yana hannunka.


Da na tuna da wannan, sai na sa zuciya ga gaba.


Ya Ubangiji, na kawo kuka gare ka na neman taimako, Ya Ubangiji, kai ne mai kiyaye ni, Kai kaɗai nake so a rayuwata duka.


Ubangiji yana kiyaye masu tsoronsa, Waɗanda suke dogara ga madawwamiyar ƙaunarsa.


Amma wanda yake wajen Yakubu ba haka yake ba, Domin shi ne ya halicci dukan abu, Isra'ila kuwa abin mallakarsa ne, Ubangiji Mai Runduna ne sunansa.


Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali, Dukanku da kuke sa zuciya ga Ubangiji!


Gama shi ba kamar waɗannan yake ba, Shi na Yakubu ne. Shi ne ya yi dukan kome, Kabilan Isra'ilawa gādonsa, Sunansa Ubangiji Mai Runduna.


To gare shi ne kuka gaskata da Allah, wanda ya ta da shi daga matattu, ya kuma ɗaukaka shi, domin bangaskiyarku da begenku su kasance ga Allah.


Ishaya kuma ya ce, “Tsatson Yesse zai bayyana, Wanda zai tashi yă mallaki al'ummai, A gare shi ne al'ummai za su sa zuciya.”


Ya Isra'ila, ki dogara ga Ubangiji, Saboda ƙaunarsa madawwamiya ce, A koyaushe yana da nufin yin gafara.


Masu farin ciki ne waɗanda suka dogara gare ka, Ya Allah Mai Runduna!


Ya jama'ata, ku dogara ya Allah a kowane lokaci! Ku faɗa masa dukan wahalarku, Gama shi ne mafakarmu.


Me ya sa nake baƙin ciki? Me ya sa nake damuwa? Zan dogara ga Allah, Zan ƙara yabonsa, Mai Cetona, Allahna.


Na fid da zuciya ɗungum. To, in Allah ya kashe ni, sai me? Zan faɗa masa ƙarata.


Aka taimake su yin yaƙi da abokan gābansu, sai aka ba da Hagarawa da duk waɗanda suke tare da su a hannunsu, saboda suka yi roƙo ga Allah a cikin yaƙin, Allah kuwa ya amsa musu roƙonsu saboda sun dogara gare shi.


Dawuda kuwa ya damu ƙwarai gama mutane suna niyyar su jajjefe shi da duwatsu, domin ransu ya ɓace saboda 'ya'yansu mata da maza. Amma Ubangiji Allahnsa ya ƙarfafa shi.


Kai kaɗai nake so, ya Ubangiji, Na yi alkawari in yi biyayya da dokokinka.


Me ya sa ni ɓacin rai haka? Me ya sa ni damuwa? Zan dogara ga Allah. Har yanzu ma zan yabe shi, Mai Cetona, Allahna.


Me ya sa nake baƙin ciki haka? Me ya sa nake damuwa ƙwarai? Zan dogara ga Allah, Zan sāke yin yabonsa, Mai Cetona, Allahna.


Ba za su sami gādo tare da 'yan'uwansu ba, Ubangiji ne gādonsu kamar yadda ya alkawarta musu.


Bari Allah Mai Iko Dukka ya zama zinariyarka, Ya zama azurfa, wadda aka tula dominka.


A koyaushe zan sa zuciya gare ka, Zan yi ta yabonka.


Sa'ad da nake alhini, ina cikin damuwa, Ka ta'azantar da ni, ka sa in yi murna.


Amma ni zan kafa ido ga Ubangiji, Zan jira ceton Allahna, Allahna zai ji ni.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ