Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ƙidaya 23:8 - Littafi Mai Tsarki

8 Ƙaƙa zan iya la'anta wanda Allah bai la'antar ba? Ƙaƙa zan iya tsine wa wanda Ubangiji bai tsine wa ba?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Yaya zan iya la’anta waɗanda Allah bai la’anta ba? Yaya zan tsine waɗanda Ubangiji bai tsine ba?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ƙidaya 23:8
8 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ba wata maitar da za ta cuci Yakubu, Ba kuwa sihirin da zai cuci Isra'ilawa. Yanzu za a ce, ‘Duba irin abin da Allah ya yi domin Yakubu, wato Isra'ilawa!’


Na sa masu duba su zama wawaye, Na sassāke annabce-annabcen masanan taurari. Na bayyana kuskuren maganar masu hikima, Na kuma nuna masu hikimarsu wauta ce.


Ga shi, an umarce ni in sa albarka. Ya sa albarka, ba zan iya janye ta ba.


Allah kuwa ya ce wa Bal'amu, “Ba za ka tafi tare da su ba, ba kuwa za ka la'anta su ba, gama albarkatattu ne su.”


Ina roƙonka, ka zo yanzu, ka la'anta mini mutanen nan, gama sun fi ƙarfina, ko ya yiwu in ci su, in kore su daga ƙasar, gama na sani duk wanda ka sa wa albarka zai albarkatu, wanda kuwa ka la'anta, zai la'antu.”


Bal'amu kuwa ya faɗi jawabinsa, ya ce “Tun daga Aram Balak ya kawo ni, Shi Sarkin Mowab ne daga gabashin duwatsu. ‘Zo, la'anta mini Yakubu, Zo, ka tsine wa Isra'ila!’


La'ana ba za ta kama ka ba, sai dai in ka cancance ta. Tana kamar tsuntsayen da suke firiya da dare ba za su sauka ba.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ