Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ƙidaya 21:28 - Littafi Mai Tsarki

28 Gama sojojin Sihon sun shiga kamar wuta, A wannan birni na Heshbon, Sun cinye Ar ta Mowab, Ta murƙushe tuddan Arnon.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

28 “Mayaƙansa sun fito kamar harshen wuta suka ƙone birnin Ar na Mowab suna hallaka ’yan ƙasar tuddan Arnon.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ƙidaya 21:28
20 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.”


Saboda haka zan aukar da wuta a kan Yahuza Ta ƙone kagarar Urushalima.”


Zan aukar da wuta a ƙasar Mowab, Ta ƙone kagarar Keriyot. Jama'ar Mowab za su mutu a hargitsin yaƙi, Sa'ad da sojoji suke sowa, ana busa ƙahoni.


Saboda haka zan aukar da wuta a kan garun Rabba, Ta ƙone kagarar birnin. Za a yi kururuwa a ranar yaƙi, Faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.


Saboda haka zan aukar da wuta a kan Teman, Ta ƙone kagarar Bozara.”


Saboda haka zan aukar da wuta a kan garun Taya, Ta ƙone kagarar birnin.”


Saboda haka zan aukar da wuta a kan garun Gaza ta ƙone kagarar birnin.


Don haka zan aukar da wuta a kan fādar Sarkin Suriya. Za ta ƙone kagarar Ben-hadad, sarki.


Ubangiji Mai Runduna zai aukar da cuta don ya hukunta waɗanda suke ƙosassu yanzu. Za su ji jikinsu na ta ƙuna kamar wuta.


Amma idan ba haka yake ba, Allah ya sa wuta ta fito daga wurin Abimelek ta cinye mutanen Shekem da na Bet-millo. Bari Allah ya sa kuma wuta ta fito daga wurin mutanen Shekem da na Bet-millo ta cinye Abimelek.”


‘Yau za ku ratsa kan iyakar ƙasar Mowab a Ar.


“Sai Ubangiji ya ce mini, ‘Kada ku dami Mowabawa, ko kuwa ku tsokane su, gama ba zan ba ku ƙasarsu ku mallake ta ba. Na riga na bayar da Ar ta zama mallakar zuriyar Lutu.’ ”


Kashegari, sai Balak ya ɗauki Bal'amu ya kai shi kan Bamotba'al, daga can ya ga rubu'in mutanen.


Domin haka mawaƙa sukan ce, “Ku zo Heshbon, bārin sarki Sihon! Muna so mu ga an sāke gina an kuma fanso shi.


Aka karkashe samari a cikin yaƙi, 'Yan mata kuma suka rasa ma'aura.


Mutanen Heshbon da na Eleyale suka yi kuka da ƙarfi, har ana iya jin kukansu daga Yahaza. Har mayaƙa ma sun yi rawar jiki, zuciyarsu ta karai.


Mutanen Mowab sun gajiyar da kansu da zuwa wurin matsafarsu na kan dutse da masujadarsu, suna addu'a, amma ba zai amfana musu kome ba.


Itacen ƙaya kuwa ya ce wa itatuwan, ‘In da gaske kuke, kuna so ku naɗa ni sarkinku, to, sai ku zo, ku fake a inuwata, in ba haka ba kuwa, bari wuta ta fito daga itacen ƙaya ta cinye itacen al'ul na Lebanon.’ ”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ