Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Karin Magana 3:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Ɗana kada ka manta da abin da na koya maka. Kullum ka tuna da abin da na faɗa maka ka yi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Ɗana, kada ka manta da koyarwata, amma ka kiyaye umarnaina a cikin zuciyarka,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Karin Magana 3:1
31 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ka nemi hikima da basira! Kada ka manta ko ka ƙyale abin da na faɗa.


Ina murna da dokokinka, Ba zan manta da umarnanka ba.


Ɗana, ka kasa kunne ga koyarwar mahaifinka, ka mai da hankali ga abin da mahaifiyarka take faɗa.


Faufau ba zan raina ka'idodinka ba, Gama saboda su ka bar ni da rai.


Ka fassara mini dokarka, ni kuwa zan yi biyayya da ita, Zan kiyaye ta da zuciya ɗaya.


Amma wannan shi ne alkawarin da zan yi da mutanen Isra'ila bayan waɗancan kwanaki, ni Ubangiji na faɗa. Zan sa dokokina a cikinsu, zan rubuta su a zukatansu, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama jama'ata.


Na riƙe maganarka a zuciyata, Don kada in yi maka zunubi.


“Sai ku lura, ku aikata dukan umarnan da na umarce ku da su don ku rayu, ku riɓaɓɓanya, ku shiga ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba kakanninku.


Ka dubi wahalata, ka cece ni, Gama ban ƙi kulawa da dokarka ba.


Mutanena sun lalace saboda jahilci. Tun da yake sun ƙi ilimi, Ni ma na ƙi ku da zaman firist ɗina. Tun da yake kun manta da umarnan Allahnka, Ni ma zan manta da 'ya'yanku.


“Sai ku lura, ku kiyaye kanku sosai, don kada ku manta da abubuwan da kuka gani da idonku kada kuma su fita a ranku dukan kwanakinku. Ku sanar wa 'ya'yanku da jikokinku da su,


Ina kai da kawowa kamar ɓatacciyar tunkiya, Ka zo ka neme ni, ni bawanka, Saboda ban ƙi kulawa da dokokinka ba.


Saboda haka, ku lura fa, kada ku manta da alkawarin da Ubangiji Allahnku ya yi da ku, don haka kada ku sassaƙa wa kanku wata siffar kowane irin kamanni wanda Ubangiji Allahnku ya hana ku.


don kada su sha su manta da doka, su kuma kauce wa gaskiya a shari'ar waɗanda aka zalunta.


Ya Urushalima, ki farka! Ki tashi da kanki, ki miƙe! Kika sha ƙoƙon hukunci wanda Ubangiji, cikin fushinsa, ya ba ki ki sha, Kika shanye shi, ya kuwa sa ki yi tangaɗi!


Amma nakan gwada madawwamiyar ƙaunata ga dubban tsararrakin da suke ƙaunata, masu kiyaye dokokina.


Zan ba su tsawon rai lada, Hakika kuwa zan cece su.”


Mugaye sun ɗaure ni tam da igiyoyi, Amma ba zan manta da dokarka ba.


Ɗana, ka koyi abin da nake koya maka, sam kada ka manta da abin da na faɗa maka ka yi.


Abin da nake koya muku, abu mai kyau ne, saboda haka ku tuna da shi duka.


Furfurar tsufa rawanin daraja ce, sakamako ne ga ran mai adalci.


Ɗana ka mai da hankali sosai, irin zamana ya zamar maka kyakkyawan misali.


“ ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka domin ka yi tsawon rai, ka sami zaman lafiya a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.


Sai ku bi hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku don ku rayu, ku zauna lafiya, ku yi tsawon rai a ƙasar da za ku mallaka.”


Kada ka kuskura su rabu da kai, ka tuna da su, ka ƙaunace su.


Ku kasa kunne! Hikima tana kira. Tana so a ji ta.


Hikima ta gina gidanta, ta yi masa ginshiƙai bakwai.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ