Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 9:4 - Littafi Mai Tsarki

4 Gama ka karya karkiyar da ta nawaita musu, Da kuma sandan da ake dukan kafaɗunsu da shi. Kai ne, ya Ubangiji, ka kori al'ummar Da ta zalunci jama'arka, ta kuma zambace su, Daidai da yadda dā ka kori rundunar sojojin Madayana tuntuni.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

4 Gama kamar yadda yake a kwanakin da aka ci Midiyan da yaƙi, kuka ji tsoro nauyin da ya nawaita musu, sandar da yake a kafaɗunsu, sandar masu zaluncinsu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 9:4
24 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Zan hallaka Assuriyawa a ƙasata ta Isra'ila, in tattake su a kan duwatsuna. Zan 'yantar da jama'ata daga karkiyar Assuriyawa, daga nauyin da suka tilasta musu su ɗauka.


Ubangiji Mai Runduna ya ce, “A wannan rana zan karya karkiya da take a wuyansu, in cire musu ƙangi, ba kuma za su ƙara zama bayin baƙi ba.


Yanzu zan karya karkiyarsa daga wuyanka, Zan kuma tsinke sarƙarta.”


Adalci da gaskiya za su ƙarfafa ki. Za ki tsira daga shan zalunci da razana. Gama ba za su kusace ki ba.


Zan sa masu zaluntarku su karkashe juna, Za su yi māye, da kisankai, da fushi. Sa'an nan dukan 'yan adam za su sani, ni ne Ubangiji, Wanda ya cece ku, ya fanshe ku. Za su sani ni ne Allah Mai Iko Dukka na Isra'ila.”


Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, don kada ku zama bayinsu. Na karya ikonsu da yake danne ku, na bar ku ku yi tafiya a sake.”


Ta wurin takobinka za ka rayu Za ka yi wa ɗan'uwanka barantaka, Amma sa'ad da ka ɓalle, Za ka kakkarye karkiyarsa daga wuyanka.”


Ubangiji ya ce, “Assuriya! Ina yin amfani da Assuriya kamar kulki don in hukunta waɗanda nake fushi da su.


Ba a koyaushe mugaye za su yi mulki a ƙasar jama'ar Allah ba, Idan kuwa suka yi, to, ya yiwu jama'ar Allah su yi laifi.


Kuna mantawa da Ubangiji wanda ya halicce ku, Wanda ya shimfiɗa sammai, Ya kuma kafa harsashin ginin duniya? Don me za ku yi ta jin tsoron fushin waɗanda suke zaluntarku, Da waɗanda suke shiri su hallaka ku? Fushinsu ba zai taɓa yi muku kome ba!


Na yi fushi da mutanena, Na maishe su kamar su ba nawa ba ne. Na sa su a ƙarƙashin ikonki, Ba ki kuwa yi musu jinƙai ba, Har da tsofaffi ma kin ba su wuya.


“Na ɗauke muku kayayyaki masu nauyi da kuke ɗauke da su a kā, Na sa kuka ajiye kwandunan aikinku.


Takalman sojojin da suka kawo yaƙi Da dukan tufafinsu da suka birkiɗe da jini, Za a ƙone su da wuta!


Ku bar mu mu zauna ƙasarku. Ku kāre mu daga masu neman hallaka mu.” Zalunci da hallakarwa za su ƙare, masu lalatar da ƙasar za su ƙare.


Ki kakkaɓe kanki, ya Urushalima! Ki tashi daga cikin ƙura, Ki hau gadon sarautarki. Ki ɓaɓɓale sarƙoƙin da suke ɗaure da ke, Ke kamammiyar jama'ar Sihiyona!


“Ku yi makoki dominta, ku da kuke kewaye da ita, Dukanku da kuka san sunanta, ku ce, ‘Ƙaƙa sandan sarauta mai iko Da sanda mai daraja ya karye?’


Ubangiji Mai Runduna zai aukar da cuta don ya hukunta waɗanda suke ƙosassu yanzu. Za su ji jikinsu na ta ƙuna kamar wuta.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ