Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 8:17 - Littafi Mai Tsarki

17 Ubangiji ya ɓoye kansa daga jama'arsa, amma ni na dogara gare shi, na kafa zuciyata a gare shi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

17 Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 8:17
39 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Gama har yanzu wahayin yana jiran lokacinsa, Yana gaggautawa zuwa cikarsa, Ba zai zama ƙarya ba. Ka jira shi, ko da ka ga kamar yana jinkiri, Hakika zai zo, ba zai makara ba.


Sa'ad da wannan ya faru, kowa zai ce, “Shi Allahnmu ne! Mun dogara gare shi, ya kuwa cece mu. Shi ne Ubangiji. Mun dogara gare shi, yanzu kuwa muna da farin ciki domin ya cece mu!”


Ga Ubangiji muke sa zuciya, Shi mai taimakonmu ne, mai kiyaye mu.


Na juya, na rabu da ke da fushi na ɗan lokaci, Amma zan nuna miki ƙaunata har abada.” Haka Ubangiji mai fansarki ya faɗa, shi wanda ya cece ki.


shi Almasihu ma, da aka miƙa shi hadaya sau ɗaya tak, domin ya ɗauke zunuban mutane da yawa, zai sāke bayyana, bayyana ta biyu, ba a kan maganar kawar da zunubi ba, sai dai domin yă ceci waɗanda suke ɗokin zuwansa.


Ka dogara ga Ubangiji! Ka yi imani, kada ka karai. Ka dogara ga Ubangiji!


Amma laifofinku suka raba tsakaninku da Allahnku. Zunubanku ne kuma suka sa ya juya daga gare ku don kada ya ji ku.


Ku duka da kuke tsoron Ubangiji, Kuna kuma biyayya da kalmomin bawansa, Zai yiwu hanyar da kuke bi ta yi duhu ƙwarai, Amma ku dogara ga Ubangiji, ku jingina ga Allahnku.


ku kuma saurari komowar Ɗansa daga Sama, wanda ya tasa daga matattu, wato Yesu, mai kuɓutar da mu daga fushin nan mai zuwa.


Amma ni zan kafa ido ga Ubangiji, Zan jira ceton Allahna, Allahna zai ji ni.


Sa'an nan za su yi kuka ga Ubangiji, Amma Ubangiji ba zai amsa musu ba. Zai ɓoye musu fuskarsa a wannan lokaci, Saboda mugayen ayyukansu.


Sai ku koma wurin Allahnku, Ku yi alheri, ku yi adalci, Ku saurari Allahnku kullayaumin.


Ya ce, ‘Zan ɓoye musu fuskata, Zan ga yadda ƙarshensu zai zama. Gama su muguwar tsara ce, 'Ya'ya ne marasa aminci.


Ubangiji yă tattaro hankalinku a kan ƙaunar nan ta Allah, da kuma jimirin nan na Almasihu.


Ba wanda ya juyo gare ka ya yi addu'a, ba wanda ya je gare ka neman taimako. Ka ɓuya mana, ka kuwa yashe mu saboda zunubanmu.


“Sa'ad da kuke ɗaga hannuwanku wajen yin addu'a, ba zan dube ku ba. Kome yawan addu'ar da kuka yi, ba zan kasa kunne ba domin zunubi ya ɓata hannuwanku.


“A kan me zan sa zuciya, ya Ubangiji? A gare ka nake dogara.


Muna bin nufinka, muna sa zuciya gare ka. Kai kaɗai ne bukatarmu.


Na zaƙu, ina jiran taimako daga Ubangiji, Ga maganarsa na dogara.


Nan take ita ma ta zo, ta yi wa Allah godiya, ta kuma yi maganar ɗan yaron nan ga dukan masu sauraron fansar Urushalima.


Ba wanda ya taɓa gani ko jin labarin wani Allah kamarka, wanda ya yi waɗannan ayyuka ga waɗanda suka sa zuciyarsu gare shi.


Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai. Muna sa zuciyarmu gare ka. Ka dinga kiyaye mu yau da gobe, ka kuma cece mu a lokatan wahala.


Na yi ta jiran taimakon Ubangiji, Sa'an nan ya kasa kunne gare ni, ya ji kukana.


Ka sa zuciyarka ga Ubangiji Ka kiyaye dokokinsa, Shi zai ba ka ƙarfin da za ka mallaki ƙasar, Za ka kuwa ga an kori mugaye.


Sai ya fara ta kan littattafan Musa da na dukan annabawa, ya yi ta bayyana musu abubuwan da suka shafe shi a dukan Littattafai.


Har wa yau, ya ce, “Zan dogara a gare shi.” Da kuma, “Ga ni nan, ni da 'ya'yan da Allah ya ba ni.”


“Me ya sa kake guduna? Me ya sa ka maishe ni kamar maƙiyi?


Duk da haka dai, Ubangiji yana jira ya yi muku alheri. A shirye yake ya yi muku jinƙai, domin a kullum yana aikata abin da yake daidai. Ta wurin dogara ga Ubangiji ake samun farin ciki.


Allah na Isra'ila, wanda ya ceci mutanensa, Shi ne yakan ɓoye kansa.


“Sa'ad da ake zuwa yaƙi da Kaldiyawa gidaje za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata, gama na ɓoye wa wannan birni zatina saboda dukan muguntarsu.


Idan mutum ya mutu, zai sāke rayuwa kuma? Amma zan jira lokaci mafi kyau, In jira sai lokacin wahala ya wuce.


“Ayuba, kai wane ne da za ka ce ba ka gan shi ba? Da kake cewa ƙararka tana gabansa, Jiransa kake yi?


Na yi fushi da su saboda muguntar kwaɗayinsu, don haka na buge su. Na ɓoye fuskata, na yi fushi. Amma sun yi taurinkai, sun yi ta komawa da baya, sun bi son zuciyarsu.


Dukanmu muka cika da zunubi har ayyukanmu mafi kyau ƙazamai ne duka. Saboda zunubanmu, muka zama kamar busassun ganyaye waɗanda iska take faucewa ta tafi da su.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ