Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 64:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Don me ba za ka kware sararin sama, ka sauko ba? Duwatsu za su gan ka, su girgiza saboda tsoro!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Da ma za ka tsage sammai ka sauko, ai, da duwatsu za su yi rawar jiki a gabanka!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 64:1
22 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Da fitowarsa daga ruwan sai ya ga sama ta dāre, Ruhu yana sauko masa kamar kurciya.


Sa'an nan na ga wani babban kursiyi fari, da wanda yake a zaune a kai, sai sama da ƙasa suka guje wa Zatinsa, suka ɓace.


Duniya ta girgiza, sararin sama ya kwararo ruwa, Saboda bayyanar Allah, har Dutsen Sinai ya girgiza, Saboda bayyanar Allah na Isra'ila.


Ubangiji ya ce, “Kwanaki suna zuwa, Sa'ad da girbi zai bi bayan huda nan da nan, Matsewar ruwan inabi kuma Za ta bi bayan shuka nan da nan. Duwatsu za su zubo da ruwan inabi mai zaƙi, Tuddai kuma su gudano da shi.


Ya Ubangiji, ka dube mu daga Sama, wurin da kake cike da tsarki da ɗaukaka. Ina kulawan nan da kake yi mana? Ina ikon nan naka? Ina ƙaunan nan taka da juyayin nan naka? Kada ka watsar da mu.


don haka na sauko in cece su daga hannun Masarawa, in fito da su daga cikin wannan ƙasa zuwa kyakkyawar ƙasa mai ba da yalwar abinci, wato ƙasar Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa.


An kaɓantar da sauran al'umma, mulkoki suka girgiza, Allah ya yi tsawa, duniya kuwa ta narke.


Su shirya saboda rana ta uku, gama a kan rana ta uku zan sauko a bisa dutsen Sina'i a gabansu duka.


Ubangiji Allah Mai Runduna Ya taɓi duniya, ta girgiza. Duk waɗanda suke zaune cikinta Suna baƙin ciki. Duniya duka takan hau Ta kuma gangara kamar ruwan Kogin Nilu.


Zan sa ku zama kamar abin sussuka, Wanda yake sabo, mai kaushi, mai tsini. Za ku sussuke duwatsu ku lalatar da su, Za a marmashe tuddai kamar ƙura.


Mun zama kamar ba ka taɓa zama mai mulkinmu ba, kamar mu kuma ba mu taɓa zama mutanenka ba.


A wannan rana ƙafafunsa za su tsaya a bisa Dutsen Zaitun wanda yake wajen gabas da Urushalima. Dutsen Zaitun zai tsage biyu daga gabas zuwa yamma, ya zama babban kwari. Sashi guda na dutsen zai janye zuwa wajen kudu. Ɗaya sashin kuma zai janye zuwa wajen arewa.


Don me al'ummai za su tambaye mu cewa, “Ina Allahnku?” Bari mu ga ka hukunta al'ummai Saboda sun zubar da jinin bayinka!


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ