Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 60:10 - Littafi Mai Tsarki

10 Ubangiji ya ce wa Urushalima, “Baƙi ne za su sāke gina garukanki, Sarakunansu kuma za su bauta miki. Na hukunta ki da fushina, Amma yanzu zan nuna miki alheri da jinƙai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

10 “Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 60:10
20 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ya Urushalima, baƙi za su bauta miki, Za su lura da garkunanki, Za su nome gonakinki, su gyara gonakinki na inabi.


Sarakuna za su zama kamar iyaye a gare ku, Sarauniyoyi za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna har ƙasa su ba ku girma, Da tawali'u za su nuna muku bangirma. Sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji, Dukan mai jiran taimakon Ubangiji, ransa ba zai ɓaci ba.”


Za a kuma kawo darajar al'ummai da girmansu a gare shi.


Da haskensa al'ummai za su yi tafiya. Sarakunan duniya za su kawo darajarsu a gare shi.


“Waɗanda yake nesa za su zo su gina Haikalin Ubangiji. Za ku kuwa sani Ubangiji Mai Runduna ya aiko ni wurinku. Wannan zai faru idan kun yi biyayya sosai da muryar Ubangiji Allahnku.”


Za a jawo al'ummai zuwa ga haskenki, Sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.


Rana tana zuwa sa'ad da jama'a za su raira waƙa, su ce, “Ina yabonka ya Ubangiji! A dā ka yi fushi da ni, Amma yanzu kana yi mini ta'aziyya, ba za ka ƙara yin fushi da ni ba.


Fushinsa ba ya daɗewa, Alherinsa kuwa har matuƙa ne. Mai yiwuwa ne yă zama ana kuka da dare, Amma a yi murna da safe.


Zan sa waɗansu su zama firistoci da Lawiyawa.”


Za ka tashi ka ji tausayin Sihiyona, Lokaci ya yi da za ka yi mata jinƙai, Wannan shi ne lokacin!


Ubangiji ya ce wa baƙin da suka bi shi, don su yi masa hidima, suna ƙaunar sunansa, sun kuma zama bayinsa, dukan wanda yake kiyaye ranar Asabar, bai kuwa ɓata ta ba, ya kuma cika alkawarinsa da aminci,


Ya aike ni in yi shela, Cewa lokaci ya yi Da Ubangiji zai ceci mutanensa, Ya kuma ci nasara a kan abokan gābansu. Ya aike ni domin in ta'azantar da masu makoki,


saboda haka kada ka yi fushi da mu ainun, ko ka riƙe da zunubanmu har abada, mu dai mutanenka ne, ka yi mana jinƙai.


Sai Ubangiji ya ji kishin ƙasarsa, Ya kuma ji ƙan mutanensa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ