Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 53:8 - Littafi Mai Tsarki

8 Aka kama shi, aka yanke masa shari'a, Aka tafi da shi domin a kashe shi, Ba wanda ya kula da ƙaddararsa. Aka kashe shi saboda zunubin mutanenmu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Da wulaƙanci da kuma hukunci aka ɗauke shi aka tafi. Wa kuwa zai yi maganar zuriyarsa? Gama an kawar da shi daga ƙasar masu rai; saboda laifin mutanena aka kashe shi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 53:8
15 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Domin Almasihu ma ya mutu sau ɗaya tak ba ƙari, domin kawar da zunubanmu, mai adalci saboda marasa adalci, domin ya kai mu ga Allah. An kashe shi a jiki, amma an rayar da shi a ruhu.


An yi masa ƙasƙanci har an hana masa gaskiya tasa. Wa yake iya ba da labarin zamaninsa? Domin an katse ransa daga duniya.”


Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Ai, muna da Shari'a, bisa ga Sharian nan kuwa ya wajaba a kashe shi, saboda ya mai da kansa Ɗan Allah.”


Saboda haka zan ba shi matsayi mai girma, Matsayi a cikin manyan mutane masu iko. Da yardarsa ya ba da ransa Ya ɗauki rabon masu laifi. Ya maye gurbin masu zunubi da yawa, Ya kuwa sha hukuncin da ya cancanci masu zunubi. Ya yi roƙo dominsu.”


Za ta kasance har shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu, sa'an nan za a kashe Masihan, ba zai sami kome ba. Jama'ar shugaban da zai zo za su hallaka birnin da Haikali. A ƙarshensa za a yi rigyawa, da yaƙe-yaƙe, da hallakarwa kamar yadda aka ƙaddara.


amma ga tsarkinsa na ruhu shi Ɗan Allah ne, da iko aka ayyana shi haka ta wurin tashinsa daga matattu.


Amma aka yi masa rauni saboda zunubanmu, Aka daddoke shi saboda muguntar da muka aikata. Hukuncin da ya sha ya 'yantar da mu, Dūkan da aka yi ta yi masa, ya sa muka warke.


A tituna suna ta magana a kaina, Bugaggu da giya kuwa suna raira waƙa a kaina.


Littafin asalin Yesu Almasihu, ɗan Dawuda, zuriyar Ibrahim ke nan.


An yashe ni a cikin matattu, Kamar waɗanda aka karkashe, Suna kuma kwance cikin kaburburansu, Waɗanda ka manta da su ɗungum, Waɗanda taimakonka ya yi musu nisa.


Amma ina kama da lafiyayyen ɗan rago, Wanda aka ja zuwa mayanka, Ashe, ni suke ƙulla wa munafuncin! Ni kuwa ban sani ba, da suke cewa, “Bari mu lalatar da itacen duk da 'ya'yansa. Bari mu datse shi daga ƙasar masu rai, Har da ba za a ƙara tunawa da sunansa ba.”


Ruwa ya sha kaina, Sai na ce, ‘Na halaka.’


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ