Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 52:6 - Littafi Mai Tsarki

6 Amma zuwa gaba za ku sani Ni ne Allah, wanda na yi magana da ku.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

6 Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 52:6
17 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Za ku sani ni ne Ubangiji sa'ad da na yi muku haka saboda sunana, ba saboda mugayen ayyukanku ba, ya ku mutanen Isra'ila. Ni Ubangiji Allah na faɗa.”


Allah ba kamar mutum ba ne, da zai yi ƙarya, Ba kuwa ɗan mutum ba ne, da zai tuba. Zai cika dukan abin da ya alkawarta, Ya hurta, ya kuwa cika.


Sai Ubangiji ya ce masa, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka, zan kuma yi alheri ga wanda nā yi wa alheri, in nuna jinƙai ga wanda nā yi wa jinƙai.”


A ko'ina jama'a suna yabonka, Sunanka ya game duniya duka. Kana mulki da adalci.


Sarakuna za su zama kamar iyaye a gare ku, Sarauniyoyi za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna har ƙasa su ba ku girma, Da tawali'u za su nuna muku bangirma. Sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji, Dukan mai jiran taimakon Ubangiji, ransa ba zai ɓaci ba.”


Abubuwan da na faɗa yanzu sun cika. Yanzu zan faɗa muku sababbin abubuwa, Tun kafin ma su soma faruwa.”


Na bayyana ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu a kan ni Allah Maɗaukaki ne, amma sunan nan nawa, Yahweh, ban sanasshe su ba.


Sai Musa ya ce wa Allah, “Idan na je wurin Isra'ilawa na ce musu, ‘Allah na ubanninku ya aiko ni gare ku,’ idan sun ce mini, ‘Yaya sunansa?’ Me zan faɗa musu?”


Ki haura a kan dutse mai tsayi, ke Urushalima, Ki faɗi albishir! Ki yi kira da babbar murya, ya Sihiyona, Ki faɗi albishir! Yi magana da ƙarfi, kada kuwa ki ji tsoro. Ki faɗa wa garuruwan Yahuza, Cewa Allahnsu yana zuwa!


Al'ummai da sarakuna za su lura da ke Kamar yadda uwa take lura da ɗanta. Za ki sani, ni Ubangiji, na cece ki, Allah Mai Iko Dukka na Isra'ila ya fanshe ki.


Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabcinsa, ko ɗan'uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji’ ba, gama su duka za su san ni, tun daga ƙarami har zuwa babba. Zan gafarta musu laifofinsu, ba kuwa zan ƙara tunawa da zunubansu ba.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ