Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 51:16 - Littafi Mai Tsarki

16 Na shimfiɗa sammai, Na kafa harsashin ginin duniya, Na ce wa Sihiyona, ‘Ku jama'ata ne! Na ba ku koyarwata, Na kuwa kiyaye ku da ikona.’ ”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

16 Na sa maganata a bakinka na kuma rufe ka da inuwar hannuna, Na shimfiɗa sammai, na kafa harsashen duniya, na kuma ce wa Sihiyona, ‘Ku mutanena ne.’ ”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 51:16
31 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ubangiji ya ce, “Amma ni, wannan shi ne alkawarina da su, Ruhuna da yake tare da ku, da kalmomina da na sa a bakunanku, ba za su rabu da bakunanku ba, ko daga bakunan 'ya'yanku, ko na jikokinku, tun daga wannan lokaci har abada.”


Ya sa maganata ta yi kaifi kamar takobi, Ya kiyaye ni da ikonsa. Ya sa na zama kamar kibiya Mai tsini shirayayyiya domin harbi.


Domin kuwa maganar da ka faɗa mini na faɗa musu, sun kuwa karɓa, sun kuma san hakika na fito daga wurinka ne, sun kuma gaskata kai ne ka aiko ni.


Zan tayar musu da wani annabi kamarka daga cikin 'yan'uwansu. Zan sa magana a bakinsa, zai faɗa musu duk abin da na umarce shi.


Amma wannan shi ne alkawarin da zan yi da mutanen Isra'ila bayan waɗancan kwanaki, ni Ubangiji na faɗa. Zan sa dokokina a cikinsu, zan rubuta su a zukatansu, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama jama'ata.


Ubangiji ya ce, “Kamar yadda sabuwar duniya da sabon sararin sama za su tabbata ta wurin ikona, haka zuriyarku da sunanku za su tabbata.


Sulusi ɗayan da ya ragu kuwa zan tura cikin wuta, Zan tace su da wuta kamar yadda akan tace azurfa, Zan gwada su kamar yadda akan gwada zinariya. Za su kira gare ni, Zan kuwa amsa musu, Zan ce, ‘Su jama'ata ne,’ Su kuma za su ce, ‘Ubangiji shi ne Allahnmu.’ ”


Ubangiji ya koya mini abin da zan faɗa, Domin in iya ƙarfafa marar ƙarfi. A kowace safiya yakan sa in yi marmarin jin abin da zai koya mini.


Dantsena ne ya kafa harsashin ginin duniya, Ya kuma shimfiɗa sammai. Lokacin da na kira duniya da sararin sama, Sukan zo nan da nan, su gabatar da kansu!


Amma bisa ga alkawarinsa muna jiran sababbin summai da sabuwar ƙasa a inda adalci zai yi zamansa.


Ubangiji ya ce, “Ina yin sabuwar duniya da sabon sararin sama. Abubuwa na dā za a manta da su ɗungum.


Wannan shi ne alkawarin da zan yi da jama'ar Isra'ila, Bayan kwanakin nan, in ji Ubangiji, Wato, zan sa shari'una a birnin zuciyarsu, In kuma rubuta su a allon zuciyarsu. Zan kasance Allahnsu, Su kuma su kasance jama'ata.


Domin wanda Allah ya aiko, zantuttukan Allah yake faɗa, gama Allah yana ba da Ruhu ba da iyakancewa ba.


Ubangiji ya ce wa jama'arsa, “Idan lokacin da zan cece ku ya yi, zan nuna muku alheri. Zan ji kukanku in taimake ku. Zan tsare ku in kiyaye ku, Zan kuwa yi wa dukan mutane alkawari ta wurinku. Zan bar ku ku sāke zama a ƙasarku wadda take kufai a yanzu.


Za su zama kamar itatuwan da aka daddasa a Haikalin Ubangiji, Suna ta yabanya a Haikalin Allahnmu.


Allah Madawwami, shi ne wurin zamanka, Madawwaman damatsansa suna tallafarka, Yana kore maka maƙiyanka, Ya ce, ‘Ka hallaka su!’


A sa'ad da zatina yake wucewa, zan sa ka a tsaguwar dutsen, in rufe ka da hannuna har in wuce,


Wahayin Yesu Almasihu da Allah ya ba shi ya nuna wa bayinsa abin da lalle ne zai auku ba da daɗewa ba, ya kuwa bayyana shi ta wurin aiko da mala'ikansa zuwa gun bawansa Yahaya,


Zan kawo su su zauna a Urushalima. Za su zama jama'ata, ni kuma zan zama Allahnsu da gaskiya da adalci.


Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu.


Dukan mutanenki za su yi abin da yake daidai, Za su kuwa mallaki ƙasar har abada. Ni na dasa su, ni na yi su Domin su bayyana girmana ga duka.


Ubangiji ne ya halicci sammai, Shi ne wanda yake Allah! Shi ne ya shata duniya ya kuma yi ta, Ya kafa ta, ta kahu da ƙarfi, za ta yi ƙarƙo! Bai halicce ta hamada da ba kome a ciki ba, Amma wurin zaman mutane. Shi ne wanda ya ce, “Ni ne Ubangiji, Ba kuwa wani Allah, sai ni.


Ko da duniya da dukan waɗanda yake zaune cikinta za su ɓace, Zan ƙarfafa harsashin gininta.


Domin in kawo wa masu makoki a Sihiyona Farin ciki da murna maimakon baƙin ciki, Waƙar yabo maimakon ɓacin rai. Ubangiji kansa zai lura da su, Za su ji daɗi kamar itace mai duhuwa. Kowa da kowa zai aikata abin da yake daidai, Za a yi yabon Allah saboda abin da ya yi.


Sai ka yi magana da shi. Ka kuma sa masa maganata a baka, zan kuwa kasance tare da bakinka da bakinsa. Zan kuma sanar da ku abin da za ku yi.


Zai rufe ka da fikafikansa, Za ka zauna lafiya a ƙarƙashinsu. Amincinsa zai tsare ka, ya kiyaye ka.


Salama, salama,” in ji Ubangiji, “Ga wanda yake nesa da wanda yake kusa. Zan warkar da su.


Sa'an nan Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina, ya ce mini, “Ga shi, na sa maganata a bakinka.


Zan ba su zuciyar da za su sani ni ne Ubangiji. Za su kuwa zama jama'ata, ni kuwa zan zama Allahnsu, gama za su komo wurina da zuciya ɗaya.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ