Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 51:10 - Littafi Mai Tsarki

10 Kai ne ka sa teku ta ƙafe, Ka kuma shirya hanya ta ruwa, Domin waɗanda kake cetonsu su haye.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

10 Ba kai ba ne ka busar da teku, ka busar da ruwan zurfafa masu girma, wanda ya yi hanya a cikin zurfafan teku saboda fansassu su ƙetare?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 51:10
20 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Tuntuni Ubangiji ya shirya hanya ta cikin teku, Da turba kuma a cikin ruwa.


“Don me mutanena ba su amsa ba Sa'ad da na je wurinsu domin in cece su? Don me ba su amsa ba sa'ad da na yi kiransu? Ba ni da isasshen ƙarfin da zan fanshe su ne? Ina da iko in sa teku ya ƙafe ta wurin umarnina, Ina kuma da iko in sa rafuffukan ruwa su zama hamada, Kifayen da suke ciki su mutu saboda rashin ruwa.


Da tabbatacciyar ƙaunarka, ka bi da jama'arka da ka fansa, Ka bi da su da ƙarfinka zuwa tsattsarkan mazauninka.


Zan lalatar da tuddai da duwatsu, In kuma busar da ciyawa da itatuwa, Zan mai da kwaruruka inda akwai rafi hamada, In kuma busar da kududdufan ruwa.


Da ƙarfin ikonka ka raba teku, Ka farfashe kawunan dodannin ruwa,


Ka yi tafiya a teku, Ka haye teku mai zurfi, Amma ba a ga shaida inda ka taka ba.


Ya tsauta wa Bahar Maliya, ta ƙafe, Har ya bi da jama'arsa su haye Kamar a bisa busasshiyar ƙasa.


Ya cece su daga maƙiyansu, Ya ƙwato su daga wurin abokan gābansu.


Ubangiji zai kawo iska mai zafi wadda za ta busar da Kogin Nilu, da na Yufiretis. Zai bar ƙananan rafuffuka bakwai ne kaɗai, don kowa da kowa ya taka ya haye.


Za a yi babbar karauka daga Assuriya domin sauran mutanen Isra'ila da suka ragu a can, kamar yadda aka yi wa kakanninsu sa'ad da suka bar Masar.


Za a yi babbar karauka a can, Za a kira ta, “Hanyar Tsarki.” Ba mai zunubi da zai taɓa bi ta wannan hanya, Ba wawayen da za su ruɗar da waɗanda suke tafiya can.


Ba za a sami zakoki a can ba, Mugayen namomin jeji ba za su bi ta can ba. Waɗancan da Ubangiji ya fansar Su za su zo gida ta wannan hanya.


Za a ce da ku, “Tsattsarkar Jama'ar Allah,” “Jama'ar da Ubangiji ya Fansa!” Za a kira Urushalima, “Birnin da Allah yake Ƙauna,” “Birnin da Allah bai Yashe shi Ba.”


daga dukan wahalar da suke sha. Ba mala'ika ne ya cece su ba, amma Ubangiji ne. Da ƙaunarsa da juyayinsa ya fanshe su. A koyaushe yake lura da su a dā,


Za su bi ta cikin tekun wahala, Zan kwantar da raƙuman teku, Kogin Nilu zai ƙafe duk da zurfinsa, Za a ƙasƙantar da Assuriya, Sandan sarautar Masar zai rabu da ita.


Amma Isra'ilawa suka yi tafiya a busasshiyar ƙasa a tsakiyar bahar, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu.


Za su kai Urushalima da murna, Suna raira waƙa suna sowa don murna. Za su yi farin ciki har abada, Ba damuwa da ɓacin rai har abada.


“Zan nuna muku abubuwa masu banmamaki, Kamar a kwanakin da kuka fito ƙasar Masar.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ