Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 50:4 - Littafi Mai Tsarki

4 Ubangiji ya koya mini abin da zan faɗa, Domin in iya ƙarfafa marar ƙarfi. A kowace safiya yakan sa in yi marmarin jin abin da zai koya mini.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

4 Ubangiji Mai Iko Duka ya ba ni harshen umarni, don in san maganar da za tă ƙarfafa gajiyayye. Ya farkar da ni da safe, ya farkar da kunnena don in saurara kamar wanda ake koya masa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 50:4
31 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Domin ni ne zan ba ku ikon hurci, da kuma hikima wadda duk abokan adawarku, ba za su iya shanyewa ko musawa ba.


Sa'an nan Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina, ya ce mini, “Ga shi, na sa maganata a bakinka.


Manufar da aka bayyana sosai kamar zubin zinariya take wanda aka yi a kan azurfa.


Me ya fi wannan zama abin murna? Mutum ya sami maganar da take daidai a lokacin da ya dace!


Tun kafin fitowar rana ina kira gare ka neman taimako, Na sa zuciya ga alkawarinka.


A gare ka nake dogara, Da safe ka tuna mini da madawwamiyar ƙaunarka. Addu'ata ta hau zuwa gare ka, Ka nuna mini hanyar da zan bi.


A gare ka zan yi addu'a, ya Ubangiji, Da safe za ka ji muryata, Da hantsi zan yi addu'ata, In kuma jira amsa.


Duk suka yabe shi, suna mamakin maganarsa ta alheri da ya faɗa, har suka ce, “Ashe, wannan ba ɗan Yusufu ba ne?”


Da ya zo garinsu, ya koya musu a majami'arsu, har suka yi mamaki, suka ce, “Daga ina mutumin nan ya sami wannan hikima haka, da kuma mu'ujizan nan?


Ku zo gare ni dukanku masu wahala, masu fama da kaya, ni kuwa zan hutasshe ku.


Ba kuwa wanda ya iya tanka masa. Daga ran nan kuwa ba wanda ya yi ƙarfin halin sāke tambayarsa wani abu.


Sai dogaran suka amsa suka ce, “A'a, ba mutumin da ya taɓa magana kamar wannan!”


Kai ne mafi kyau a cikin dukan mutane, Kai mai kyakkyawan lafazi ne, Kullum Allah yakan sa maka albarka!


Ya Ubangiji, ina kira gare ka, neman taimako, Kowace safiya nakan yi addu'a gare ka.


Damuwa takan hana wa mutum farin ciki, amma kalmomin alheri za su sa shi ya yi murna.


Almajiraina su ne za su lura, su kuma kiyaye jawabin da Allah ya ba ni.


Suna gunaguni a kaina suna cewa, “Su wa wannan mutum yake tsammani yana koya musu? Wa yake bukatar jawabinsa? Sai ga 'yan yaran da aka yaye kaɗai yake da amfani!


Za ta yi ta auko muku a kai a kai kowace safiya. Tilas ku sha ta dare da rana. Kowane sabon jawabin da zai zo muku daga wurin Allah, zai kawo muku sabuwar razana!


Makaho zai iya ganin gari, Kurma kuma zai iya ji.


Yakan ƙarfafa masu kasala da masu jin gajiya.


Ku duka da kuke tsoron Ubangiji, Kuna kuma biyayya da kalmomin bawansa, Zai yiwu hanyar da kuke bi ta yi duhu ƙwarai, Amma ku dogara ga Ubangiji, ku jingina ga Allahnku.


“Ni kaina zan koya wa mutanenki, Zan kuwa ba su wadata da salama.


Gama zan biya bukatar waɗanda suka gaji, in wartsakar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”


“Kowace safiya za a yi hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji da ɗan rago bana ɗaya marar lahani.


Ubangiji kuwa ya ce mini, ‘Abin da suka faɗa daidai ne.


Zan tayar musu da wani annabi kamarka daga cikin 'yan'uwansu. Zan sa magana a bakinsa, zai faɗa musu duk abin da na umarce shi.


Idan wani ya yi tuntuɓe, Ya gaji, ya rasa ƙarfi, Kalmominka suka ƙarfafa zuciyarsa, Har ya iya tsayawa kyam.


Sai na amsa, “Ga ni, umarnanka zuwa gare ni Suna a Littafin Shari'a.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ