Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 5:18 - Littafi Mai Tsarki

18 Kun shiga uku! Ba ku iya kuɓuta daga zunubanku ba.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

18 Kaiton waɗanda suke jan zunubi da igiyar ruɗu, da kuma mugunta da igiyoyin keken yaƙin,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 5:18
23 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Amma cikin annabawa na Urushalima, Na ga abin banƙyama. Suna yin zina, suna ƙarya, Suna ƙarfafa hannuwan masu aikata mugunta, Saboda haka ba wanda ya juya ga barin muguntarsa, Dukansu suna kama da Saduma, Mazaunanta kuwa kamar Gwamrata.”


“Kun karya zuciyar adali ta wurin ƙaryarku, ko da yake ni ban karya zuciyarsa ba. Kun ƙarfafa wa mugu gwiwa, don kada ya bar hanyarsa ta mugunta, ya tsira.


Gama ƙasar cike take da mazinata, Saboda la'ana, ƙasar za ta yi makoki, Wuraren kiwo na jeji sun bushe, Manufarsu mugunta ce, Ba su mori ƙarfinsu a inda ya kamata ba.


Annabawa sun yi annabcin ƙarya, Firistoci kuma sun yi mulki da ikon kansu, Mutanena kuwa suna so haka! Amma sa'ad da ƙarshe ya zo, me za ku yi?”


Domin yana ganin kansa shi wani abu ne, A tsammaninsa Allah ba zai tona asirinsa ba, Ya hukunta zunubinsa.


“To, ni kaina ma a dā na ga kamar wajibi ne in yi abubuwa da yawa, na gāba da sunan Yesu Banazare.


Za su fisshe ku daga jama'a. Hakika, lokaci ma na zuwa da kowa ya kashe ku, zai zaci bautar Allah yake yi.


“A lokacin nan, Zan bincike Urushalima da fitilu, Zan kuwa hukunta marasa kulawa Waɗanda suke zaman annashuwa, Waɗanda suke cewa a zukatansu, ‘Ubangiji ba zai yi alheri ba, Ba kuma zai yi mugunta ba!’


“Mutum ya iya ɓoye kansa a wani lungu Inda ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji. “Ashe, ban cika sammai da duniya ba?


Kuna fāriya a kan alkawarin da kuka yi da mutuwa, kun ƙulla yarjejeniya da lahira. Kun tabbata masifa za ta ƙetare ku sa'ad da ta zo, domin kun dogara ga ƙarairayi da ruɗi don su kiyaye ku.


Wawaye sukan ce wa kansu, “Ba Allah!” Dukansu sun lalace, sun aikata mugayen al'amura, Ba wanda yake aikata abin da yake daidai.


Mugun mutum yakan ce wa kansa, “Allah bai kula ba! Ya rufe idonsa, ba zai taɓa ganina ba.”


Sa'an nan Mika ya ce, “Yanzu na sani Ubangiji zai sa mini albarka, da yake na sami Balawe ya zamar mini firist.”


Mika kuwa yana da ɗakin gumaka. Ya yi gumaka, da falmaransu, da kan gida. Ya keɓe ɗaya daga cikin 'ya'yansa maza domin ya zama firist nasa.


Da Yehudi ya karanta sakin layi uku ko huɗu sai sarki ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone littafin duka.


Mugunta da ta'adi kamar ci da sha suke a gare su.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ