Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 49:25 - Littafi Mai Tsarki

25 Ubangiji ya amsa ya ce, “Wannan shi ne ainihin abin da zai faru. Za a ƙwace kamammun yaƙi, Za a kuma ƙwace wason da masu baƙin mulki ya yi. Zan yi yaƙi da dukan wanda yake yaƙi da ku, Zan kuwa kuɓutar da 'ya'yanku.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

25 Amma ga abin da Ubangiji yana cewa, “I, za a ƙwace kamammu daga jarumawa, a kuma karɓe ganima daga hannun marasa tsoro; zan gwabza da waɗanda suke gwabzawa da ke, zan kuwa ceci ’ya’yanki.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 49:25
39 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ku faɗa wa dukan wanda ya karai, ku ce, “Ka ƙarfafa, kada kuwa ka ji tsoro! Allah yana zuwa domin ya kuɓutar da kai, Yana zuwa domin ya ɗauki fansa a kan abokan gābanka.”


“Ni kaina zan koya wa mutanenki, Zan kuwa ba su wadata da salama.


Ga annobar da Ubangiji zai bugi dukan al'ummai da ita, wato su da suka tafi su yi yaƙi da Urushalima. Naman jikunansu zai ruɓe lokacin da suke a tsaye. Idanunsu kuma za su ruɓe cikin kwarminsu. Harsunansu za su ruɓe a bakunansu.


Al'ummai da yawa za su taimaki jama'ar Isra'ila su koma ƙasarsu wadda Ubangiji ya ba su. A can sauran al'umma za su yi wa Isra'ila hidima kamar bayi. Waɗanda suka kama Isra'ilawa a dā yanzu Isra'ilawa za su kama su. Jama'ar Isra'ila za ta mallaki waɗanda suka taɓa zaluntarsu.


A lokacin nan zan 'yantar da ku daga mulkin Assuriya, karkiyarsu ba za ta ƙara zama kaya mai nauyi a wuyanku ba.”


Waɗanda suka sa maka albarka zan sa musu albarka, amma zan la'anta waɗanda suka la'anta ka. Dukan al'umman duniya za su roƙe ni in sa musu albarka kamar yadda na sa maka.”


Duk mai aikata zunubi, na Iblis ne, don tun farko Iblis mai aikata zunubi ne. Dalilin bayyanar Ɗan Allah shi ne domin yă rushe aikin Iblis.


Ubangiji ya ce, “Ke kuma, saboda jinin alkawarina da yake tsakanina da ke, Zan 'yantar da waɗanda suke cikin rami, Waɗanda aka kama daga cikinki.


“Ubangiji ya ce, ‘Sa'ad da kuka cika shekara saba'in a Babila, zan ziyarce ku, zan kuwa cika muku alkawarina. Zan komo da ku zuwa wannan wuri.


Sa'ad da wannan ya faru, kowa zai ce, “Shi Allahnmu ne! Mun dogara gare shi, ya kuwa cece mu. Shi ne Ubangiji. Mun dogara gare shi, yanzu kuwa muna da farin ciki domin ya cece mu!”


Ki yi farin ciki saboda an yi masa haka, ya sama! Ku yi farin ciki, ku tsarkaka da manzanni da annabawa, domin Allah ya rama muku abin da ya yi muku!”


Amma Urushalima ta sama, ai 'ya ce, ita ce kuma uwarmu.


Sa'an nan Ubangiji zai tafi ya yi yaƙi da waɗannan al'ummai kamar yadda ya yi a dā.


Ba mai iya shiga gidan ƙaƙƙarfan mutum ya washe kayansa, sai ko ya fara ɗaure ƙaƙƙarfan mutumin, sa'an nan kuma ya washe gidansa.


Ka yi hamayya da masu hamayya da ni, ya Ubangiji, Ka yi faɗa da masu faɗa da ni!


Sojojinsu na ruri kamar zakunan da suka kashe nama, suna kuwa ɗauke da shi don kada wani ya ƙwace musu.


Na aiki Assuriya ta faɗa wa al'ummar da ba ta tsoron Allah, da yaƙi, wato jama'ar da ta sa na yi fushi. Na aike su su yi waso su yi sata, su tattake jama'a kamar ƙura a tituna.”


Ubangiji zai sāke yi wa jama'arsa Isra'ila jinƙai, ya zaɓe su su zama nasa. Zai sāke sa su zauna a ƙasarsu, baƙi ma za su zo su zauna tare da su.


Za su zama alamu na kasancewar Ubangiji Mai Runduna a Masar. Sa'ad da aka zalunci mutanen da suke can, za su yi kira ga Ubangiji su nemi taimako, zai aika musu wanda zai kuɓutar da su.


Matalauta da 'yan ƙaƙa naka yi sun sheƙa zuwa wurinka, Sun sami zaman lafiya a lokatan wahala. Ka ba su mafaka daga hadura, Ka inuwantar da su daga matsanancin zafi. Mugaye sukan tasar musu kamar hadirin ƙanƙara,


Dukan kayayyakin waɗannan jiragen ruwa ba su da amfani, tafiyarsu ba za ta yi nisa ba! Za a kwashe dukan dukiyar sojojin abokan gāba. Za ta yi yawa har sauran jama'a za su sami rabonsu. Ubangiji kansa shi zai zama sarkinmu, zai mallake mu, ya kiyaye mu.


Ka ƙarfafa jama'ar Urushalima. Ka faɗa musu sun sha wahala, ta isa, Yanzu kuwa an gafarta musu zunubansu. Na yi musu cikakken hukunci saboda dukan zunubansu.”


Ubangiji Allahnku ya kāre ku ya ce, “Ina ɗauke ƙoƙon da na ba ku cikin fushina. Ba za ku ƙara shan ruwan inabin da zai sa ku yi tangaɗi ba.


Zan kuɓutar da kai daga hannun mugaye, Zan ɓamɓare ka daga hannun marasa tausayi.”


“Ga shi, ina gāba da ke. Ni Ubangiji Allah Mai Runduna na faɗa. Zan ƙone karusanki, Takobi kuwa zai karkashe sagarun zakokinki, Zan hana miki ganima a duniya. Ba za a ƙara jin muryoyin jakadunki ba.”


Idan ba a fanshe shi ta waɗannan hanyoyi ba, sai a shekara ta hamsin ta murna, a sake shi, shi da 'ya'yansa.


'Yan sarƙa za su fita ba da jimawa ba Za su yi tsawon rai, Su kuma sami dukan abincin da suke bukata.


Gama Ubangiji ya fanshi Yakubu. Ya fanshe shi daga hannuwan waɗanda suka fi ƙarfinsa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ