Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 49:22 - Littafi Mai Tsarki

22 Ubangiji Allah ya ce wa jama'arsa, “Zan nuna alama ga al'ummai, Za su kuwa kawo 'ya'yanku gida.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

22 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, zan yi alama wa Al’ummai, zan ɗaga tutana wa mutane; za su kawo ’ya’yanki maza a hannuwansu su riƙe ’ya’yanki mata a kafaɗunsu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 49:22
20 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Za a zo daga gabas da yamma, kudu da arewa, a zauna cin abinci a Mulkin Allah.


Dukan sauran al'umma da ka halitta Za su zo su rusuna har ƙasa a gabanka. Za su yabi girmanka,


“Mutane daga kowaɗanne sassa na duniya za su girmama ni. Ko'ina za su ƙona mini halattacciyar hadaya, gama dukansu za su girmama ni,” in ji Ubangiji Mai Runduna.


Za su taho da 'yan ƙasarku daga al'ummai, su kawo mini su kyauta. Za su zo da su a tsattsarkan dutsena, wato Urushalima, za su kawo su a kan dawakai, da alfadarai, da raƙuma, da cikin karusai, kamar dai yadda Isra'ilawa suke kawo hadaya ta hatsi a Haikali cikin tsabtatattun ƙore.


Mutanena za su zo daga can nesa, Daga Birnin Sin a kudu, Daga yamma, da arewa.”


Al'ummai da yawa za su taimaki jama'ar Isra'ila su koma ƙasarsu wadda Ubangiji ya ba su. A can sauran al'umma za su yi wa Isra'ila hidima kamar bayi. Waɗanda suka kama Isra'ilawa a dā yanzu Isra'ilawa za su kama su. Jama'ar Isra'ila za ta mallaki waɗanda suka taɓa zaluntarsu.


Da ma a yi ta tunawa da sunansa har abada, Da ma shahararsa ta ɗore muddin rana tana haskakawa. Da ma dukan sauran al'umma su yabi sarkin, Dukan jama'a su roƙi Allah yă sa musu albarka, Kamar yadda ya sa wa sarki albarka.


Mulkinsa ya kai daga teku zuwa teku, Daga Kogin Yufiretis, har zuwa iyakar duniya.


Dukan al'ummai za su tuna da Ubangiji, Za su zo gare shi daga ko'ina a duniya, Dukan kabilai za su yi masa sujada.


Sa'ad da sauran al'umma da mulkoki suka taru Don su yi wa Ubangiji sujada.


Kowane mutum da yake a duniya ya kasa kunne, kowannen da yake zaune a duniya, ya duba tutar, alama da za a ɗaga sama a ƙwanƙolin duwatsu, ya kasa kunne ga busar ƙaho!


Zan faɗa wa kudu su bar su su tafi, Arewa kuma kada su riƙe su a can. Bari mutanena su komo daga manisantan ƙasashe, Daga kowane sashi na duniya.


Ku mutanen Urushalima, ku fita daga cikin birni, Ku gyara hanyoyi domin jama'arku da suke komowa! Ku shirya babbar hanya, Ku kawar da duwatsu daga hanyar! Ku sa alama domin al'ummai su sani,


su kuwa sani ni ne wanda yake hukunta musu. “Amma zan bar waɗansu, in aika da su ga al'ummai da manisantan ƙasashe inda ba a ji labarin sunan da na yi ba, ba a kuwa ga girmana da ikona ba, wato zuwa Tarshish, da Libiya, da Lidiya, duk da gwanayen maharbanta, Rosh da Tubal, da kuma Helas. Za su ba da labarin girmana ga waɗannan al'ummai.


Jama'a da yawa da al'ummai masu iko za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Mai Runduna, su kuma roƙi alherin Ubangiji.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ