Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 45:25 - Littafi Mai Tsarki

25 Ni Ubangiji, zan kuɓutar da dukan zuriyar Yakubu, Za su kuwa yi yabona.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

25 Amma a cikin Ubangiji dukan zuriyar Isra’ila za su sami adalci za su kuwa yi yabo.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 45:25
36 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Za ku watsa su sama cikin iska, Iska za ta hure su, ta tafi da su, Hadiri kuma zai warwatsar da su. Amma za ku yi murna, gama ni ne Allahnku, Za ku yabe ni, Allah Mai Tsarki na Isra'ila.


Waɗansunku ma dā haka suke, amma an wanke ku, an tsarkake ku, an kuma kuɓutar da ku, da sunan Ubangiji Yesu Almasihu, da kuma Ruhun Allahnmu.


Saboda haka, “Duk mai yin alfarma, yă yi da Ubangiji” (abin da yake a rubuce ke nan).


Waɗanda ya ƙaddarar nan kuwa, su ne ya kira. Waɗanda ya kira kuwa, su ne ya kuɓutar. Waɗanda ya kuɓutar ɗin kuwa, su ne ya ɗaukaka.


Saboda haka a yanzu, ba sauran kayarwa ga waɗanda suke na Almasihu Yesu.


To, da yake mu kuɓutattu ne ta wurin bangaskiya, muna da salama ke nan a gun Allah, ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu.


Saboda haka al'amarin ya dogara ga bangaskiya, domin yă zama bisa ga alheri, don kuma a tabbatar da alkawarin nan ga dukkan zuriyar Ibrahim, ba ga masu bin Shari'a kaɗai a cikinsu ba, har ma ga waɗanda suke da bangaskiya irin Ibrahim, shi da yake ubanmu duka.


Ta gare shi kuma, duk masu ba da gaskiya suka kuɓuta daga dukan abubuwan da ba dama Shari'ar Musa ta kuɓutar da ku.


Aikin da suka yi zai yi nasara, 'ya'yansu ba za su gamu da bala'i ba, zan sa musu albarka duk da zuriyarsu har dukan zamanai.


Zan sa wa Isra'ilawa waɗanda suke na kabilar Yahuza albarka, zuriyarsu kuma za su mallaki ƙasata da duwatsuna. Zaɓaɓɓun mutanena waɗanda suke bauta mini za su zauna a can.


Za su yi suna a cikin al'ummai, Dukan wanda ya gan su zai sani, Su ne mutanen da na sa wa albarka.”


“Za su ce ta wurina kaɗai Za a iya samun nasara da ƙarfi, Amma dukan waɗanda suka raina ni za su sha kunya.


Ba a ɓoye na yi magana ba, Ban kuwa ɓoye nufina ba. Ban ce jama'ar Isra'ila Su neme ni a kowace hanyar ruɗami ba. Ni ne Ubangiji, gaskiya kuwa nake faɗa, Ina sanar da abin da yake daidai.”


Amma Ubangiji ya ceci Isra'ila, Nasararsa kuwa za ta tabbata har abada, Mutanensa ba za su taɓa shan kunya ba.


Dukan masu adalci za su yi murna, Saboda abin da Ubangiji ya aikata. Za su sami mafaka a gare shi, Dukan mutanen kirki za su yabe shi.


“Ku yabe shi, ku bayin Ubangiji! Ku girmama shi, ku zuriyar Yakubu! Ku yi masa sujada, ku jama'ar Isra'ila!


Ya ku zuriyar bawansa Ibrahim, Ya ku zuriyar zaɓaɓɓensa Yakubu.


Don mu ne masu kaciyar ainihi, masu bauta wa Allah ta wurin Ruhu, masu taƙama da Almasihu Yesu, ba mu kuma dogara da al'amuran ganin ido,


Amma ni ko kusa ba zan yi fariya ba, sai dai a game da gicciyen Ubangijinmu Yesu Almasihu, wanda ta albarkacin mutuwarsa a kan gicciye ne na yar da sha'anin duniya, duniya kuma ta yar da sha'anina.


Amma, “Duk mai yin fahariya, ya yi fahariya da Ubangiji.”


Shi da bai san zunubi ba, Allah ya mai da shi zunubi saboda mu, domin mu mu sami adalcin Allah ta wurinsa.


ya Ubangiji ka ji daga Sama, ka shara'anta bayinka, ka hukunta mai laifin, ka ɗora masa hakkinsa a kansa, amma ka kuɓutar da mara laifin, ka sāka masa bisa ga adalcinsa.


A buɗe ƙofofin birnin, A bar amintacciyar al'umma ta shiga, Al'ummar da jama'arta take aikata abin da yake daidai.


Rana tana zuwa da Ubangiji Mai Runduna zai zama kamar rawanin furanni mai daraja ga jama'arsa da suka ragu.


Gama Allah yana kusa, Zai tabbatar da ni, marar laifi ne, Ko akwai wanda zai iya kawo ƙararraki game da ni? Bari mu je ɗakin shari'a tare! Bari ya kawo ƙararrakinsa!


Bayan shan wahalarsa, zai sāke yin murna, Zai fahimta wahalar da ya sha ba ta banza ba ce, Shi ne bawana, adali, Zai ɗauki hukuncin mutane masu yawa, Ya sa su zama mutanena amintattu.


“Rana ba za ta ƙara zama haskenki da rana ba, Ko wata ya zama haskenki da dare. Ni, Ubangiji, zan zama madawwamin haskenki, Hasken ɗaukakata zai haskaka a kanki.


Dukan mutanenki za su yi abin da yake daidai, Za su kuwa mallaki ƙasar har abada. Ni na dasa su, ni na yi su Domin su bayyana girmana ga duka.


Idan kun yi rantsuwa kuka ce, ‘Har da ran Ubangiji kuwa,’ Da gaskiya, da aminci, da adalci, Sa'an nan sauran al'umma za su so in sa musu albarka, Za su kuma yabe ni.”


A waɗannan kwanaki za a ceci mutanen Yahuza, mutanen Urushalima kuwa za su zauna lafiya. Sunan da za su sa wa Urushalima birninsu, shi ne, ‘Adalcinmu Ubangiji ne.’


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ