Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 44:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Ubangiji ya ce, “Ka saurara yanzu, ya Isra'ila, bawana, Zaɓaɓɓun mutanena, zuriyar Yakubu,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 “Amma yanzu ka saurara, ya Yaƙub, bawana, Isra’ila, wanda zaɓa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 44:1
22 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

“Amma kai, Isra'ila bawana, Kai ne jama'ar da na zaɓa, Zuriyar Ibrahim, abokina,


Ubangiji ya ce, “Kada ka ji tsoro, ya barana Yakubu, Kada kuma ka yi fargaba, ya Isra'ila, Gama zan cece ka daga ƙasa mai nisa, Zan kuma ceci zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yakubu zai komo, ya yi zamansa rai a kwance, Ba kuwa za a tsoratar da shi ba.


Zaki ya hauro daga cikin ruƙuƙinsa, Mai hallaka al'ummai ya kama hanya, Ya fito daga wurin zamansa don ya mai da ƙasarku kufai, Ya lalatar da biranenku, su zama kango, ba kowa.


“Ya mutanen Urushalima! Ya mutanen Urushalima! Masu kisan annabawa, masu jifan waɗanda aka aiko gare ku! Sau nawa ne ina so in tattaro ku kamar yadda kaza take tattara 'yan tsakinta a cikin fikafikanta, amma kun ƙi!


“Ku mutanena, ku kasa kunne yanzu, ku zo gare ni, Ku zo gare ni, za ku kuwa sami rai! Zan yi tabbataccen alkawari da ku, Zan sa muku albarkun da na alkawarta wa Dawuda.


Ya Isra'ila, Ubangiji wanda ya halicce ku ya ce, “Kada ku ji tsoro, na fanshe ku. Na kira ku da sunanku, ku nawa ne.


Ko akwai wanda zai kasa kunne ga wannan? Ko za ku kasa kunne ku yi lura daga yanzu?


“Zan kafa alkawarina da kai, da zuriyarka a bayanka cikin dukan tsararrakinsu, madawwamin alkawari ke nan, in zama Allahnka da na zuriyarka a bayanka.


Ya ba da ita ga bawansa Isra'ila, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce.


Ubangiji zai sāke yi wa jama'arsa Isra'ila jinƙai, ya zaɓe su su zama nasa. Zai sāke sa su zauna a ƙasarsu, baƙi ma za su zo su zauna tare da su.


Na kawo ka daga maƙurar duniya, Na kira ka daga kusurwoyi mafi nisa. Na ce maka, ‘Kai ne bawana.’ Ban ƙi ka ba, amma maimakon haka na zaɓe ka.


Ubangiji ya ce, “Ka tuna da waɗannan abu, ya Isra'ila, Ka tuna kai bawana ne. Na halicce ka domin ka zama bawana, Ba zan taɓa mantawa da kai ba.


Na sa ka domin ka taimaki bawana Isra'ila, Jama'ar da ni na zaɓa. Na ba ka girma mai yawa, Ko da yake kai ba ka san ni ba.


“Ku kasa kunne gare ni, ya Isra'ila, jama'ar da na kira! Ni ne Allah, farko, da ƙarshe, Allah Makaɗaici!


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ