Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 43:26 - Littafi Mai Tsarki

26 “Bari mu tafi ɗakin shari'a, ku kawo ƙararrakinku. Ku gabatar da matsalarku don a tabbatar kuna da gaskiya!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

26 Ku tunashe ni abin da ya riga ya wuce, bari mu yi muhawwara wannan batu tare; ku kawo hujjarku na nuna rashin laifinku.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 43:26
19 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ubangiji ya ce, “Yanzu fa, bari mu daidaita al'amarinmu. Duk kun yi ja wur da zunubi, amma zan wanke ku, ku yi fari fat kamar auduga. Zai yiwu zunubinku ya sa ku zama ja wur, amma za ku yi fari fat kamar farin ulu.


Kirawo sauran al'umma, su zo ga shari'a. A cikin allolinsu wane zai iya faɗar abin da yake a gaba? A cikinsu wa ya yi hurci a kan abin da yake faruwa yanzu? Bari waɗannan alloli su kawo shaidunsu Don su tabbatar daidai suke, Su shaida gaskiyar maganganunsu.


Wa zai ɗora wa zaɓaɓɓun Allah laifi? Allah ne yake kuɓutar da su!


Ka karɓi addu'ata kamar turaren ƙonawa, Ka karɓi ɗaga hannuwa sama da na yi kamar hadayar maraice.


Don saboda rashin fahimtar hanyar samun adalci, wadda Allah ya tanadar, da kuma neman kafa tāsu hanya, sai suka ƙi bin ita wannan hanya ta samun adalci wadda Allah ya tanadar.


Allah ya ce, “Ku yi shiru ku kasa kunne gare ni, ku manisantan ƙasashe! Ku yi shiri ku gabatar da ƙararku a ɗakin shari'a. Za ku sami zarafi ku yi magana. Bari mu taru mu ga wanda yake da gaskiya.


Gama Allah yana kusa, Zai tabbatar da ni, marar laifi ne, Ko akwai wanda zai iya kawo ƙararraki game da ni? Bari mu je ɗakin shari'a tare! Bari ya kawo ƙararrakinsa!


“Ina so wanda zai yi roƙo ga Allah domina, Kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.


Gama ka riga ka ce, ‘Zan yi maka alheri, in kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar yashin teku, waɗanda ba su lasaftuwa saboda yawansu.’ ”


“Wa kyauta ta shiga tsakaninsu da Allah, ya fara bayarwa, Har da za a sāka masa?”


Sai ya ce musu, “Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane. Amma Allah ya san zukatanku. Abin da mutane suke girmamawa ƙwarai, ai, abin ƙyama ne a gun Allah.


Ubangiji Allah ya ce, “Ga abin da zan sa mutanen Isra'ila su roƙe ni, in yi musu. Za su roƙe ni in yawaita su kamar garken tumaki.


Shi kuwa mutumin, don yana son baratar da kansa, ya ce wa Yesu, “To, wane ne ɗan'uwa nawa?”


Ka tashi, ya Allah, ka kāre kanka! Ka tuna fa, marasa tsoronka suna ta yi maka ba'a dukan yini!


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ