Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 37:23 - Littafi Mai Tsarki

23 Wa kake tsammani kana raina, kana yi masa ba'a? Ba ka ba ni girma ba, ni Allah mai tsarki na Isra'ila.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

23 Wane ne ka zargi ka kuma yi wa saɓo? A kan wa ka tā da muryarka ka kuma daga idanu cikin fariya? A kan Mai Tsarkin nan na Isra’ila!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 37:23
42 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Zan sanar da sunana mai tsarki a tsakiyar jama'ata, wato Isra'ila, ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, al'ummai kuwa za su sani ni ne Ubangiji Mai Tsarki a cikin Isra'ila.


Shi ne magabci, mai ɗaukaka kansa, yana gāba da duk abin da ya shafi sunan Allah, ko kuma wanda ake yi wa ibada. Har ma yakan zauna a Haikalin Allah, yana cewa, shi ne Allah.


Zai yi maganganun saɓo a kan Maɗaukaki, zai tsananta wa tsarkaka na Maɗaukaki, zai yi ƙoƙari ya sāke lokatai, da shari'a, za a kuwa bashe su a hannunsu, har shekara uku da rabi.


Har yanzu za ka ce kai allah ne a gaban waɗanda suke ji maka rauni, Ko da yake kai mutum ne kawai, ba Allah ba?


Za ku watsa su sama cikin iska, Iska za ta hure su, ta tafi da su, Hadiri kuma zai warwatsar da su. Amma za ku yi murna, gama ni ne Allahnku, Za ku yabe ni, Allah Mai Tsarki na Isra'ila.


A wannan rana, mutane za su juyo neman taimako ga Mahaliccinsu, Allah Mai Tsarki na Isra'ila.


“Dan mutum, ka faɗa wa Sarkin Taya, cewa Ubangiji Allah ya ce, “ ‘Da yake zuciyarka ta cika da alfarma, Har ka ce kai allah ne, Kana zaune a mazaunin allah, kana zaune a tsakiyar tekuna, To, kai mutum ne kawai, ba allah ba, Ko da yake ka aza kanka mai hikima ne kamar Allah.


Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Ubangiji wanda ya fanshe ku ya ce, “Domin in cece ku zan aiko sojoji gāba da Babila, Zan rushe ƙofofin birni, Sowar mutanen birnin za ta zama kuka.


Gama ni ne Ubangiji Allahnku, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, wanda ya cece ku. Zan ba da Masar, da Habasha, da Seba Ga Sairus domin fansarku.


Ubangiji ya ce, “Isra'ila, ku kima ne marasa ƙarfi kuma, Kada ku ji tsoro, zan taimake ku. Ni Allah Mai Tsarki na Isra'ila, ni ne mai fansarku.


Sarkin Assuriya ya aiko babban shugaban mayaƙansa don ya zagi Allah mai rai. Da ma Ubangiji Allahnka ya ji waɗannan zage-zage ya kuma hukunta waɗanda suka yi su. Don haka sai ka yi addu'a ga Allah saboda mutanenmu waɗanda suka ragu.”


Bari dukan waɗanda suke zaune a Sihiyona su yi sowa su raira waƙa! Gama Mai Tsarki, Allah na Isra'ila, mai girma ne, Yana zaune tare da mutanensa.”


Lokaci zai yi sa'ad da jama'ar Isra'ila da suka ragu ba za su ƙara dogara ga al'ummar da ta kusa hallaka su ba. Hakika za su dogara ga Ubangiji Allah, Mai Tsarki na Isra'ila.


Rana tana zuwa sa'ad da girmankan 'yan adam zai ƙare, zai kuma lalatar da fāriyar 'yan adam. Sa'an nan Ubangiji ne kaɗai za a ɗaukaka.


Akwai waɗansu mutane da suke yi wa jama'a ƙallon raini suna ɗaurin gira.


Kada ka manta da hargowar maƙiyanka, Kada ka manta da hayaniyar da magabtanka suke ta yi.


Amma ka tuna fa, ya Ubangiji, abokan gābanka suna yi maka ba'a, Su wawaye ne waɗanda suke raina ka.


Sukan faɗi baƙar magana a kan Allah na Sama, Su ba da umarnai na girmankai ga mutane a duniya,


Saboda dukan wulakanci, Da zagin da nake sha daga maƙiyana da abokan gābana.


Ya kuma rubuta wasiƙu, ya zargi Ubangiji Allah na Isra'ila, ya yi maganar saɓo, yana cewa, “Kamar yadda gumakan al'umman sauran ƙasashe suka kāsa ceton jama'arsu daga hannuna, haka nan kuma Allahn Hezekiya ba zai iya ceton jama'arsa daga hannuna ba.”


Wa kake tsammani ka yi wa ba'a har da zagi? Ba ka ga girmana ba, ni Allah Mai Tsarki na Isra'ila?


Mai yiwuwa ne Ubangiji Allahnka ya ji dukan maganganun da Rabshake ya yi wanda ubangidansa, Sarkin Assuriya, ya aiko don yi wa Allah mai rai ba'a. Bari Ubangiji Allahnka ya hukunta masa saboda maganganunsa, sai ka yi addu'a saboda sauran da suka ragu.”


“Ya Ubangiji, wane ne kamarka a cikin alloli? Wa yake kamarka a cikin ɗaukaka da tsarki? Mai banrazana cikin mafifitan ayyuka, mai aikata mu'ujizai.


Har yanzu kana fariya a kan jama'ata, ba ka sake su ba.


Amma Fir'auna ya ce, “Wane ne Ubangiji, har da zan ji maganarsa, in bar Isra'ilawa su tafi? Ai, ban san Ubangiji ɗin nan ba, balle in bar Isra'ilawa su tafi.”


Za a kunyatar da kowa, dukan masu girmankai za a ƙasƙantar da su.


Kun shiga uku! A tsammaninku ku masu hikima ne, masu wayo ƙwarai.


Ubangiji ya ce, “Sa'ad da na gama abin da nake yi a kan Dutsen Sihiyona da cikin Urushalima, zan hukunta Sarkin Assuriya saboda dukan kurarinsa da girmankansa.”


Allah da yake hasken Isra'ila, zai zama wuta. Allah, Mai Tsarki na Isra'ila, zai zama harshen wuta, wanda zai ƙone kowane abu rana ɗaya, har da ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya.


Za a hallaka Mowab daga zaman al'umma, Domin ta tayar wa Ubangiji.


Ya ɗaukaka kansa, har ya mai da kansa daidai da shugaban runduna. Ya hana yin hadayar ƙonawa ta yau da kullum ga Sarkin sarakuna, ya kuma rushe masa wuri mai tsarki.


Sai Dawuda ya tambayi mutanen da suke kusa da shi, ya ce, “Me za a yi wa wanda ya kashe Bafilisten nan, har ya kawar da zargi daga Isra'ila? Gama wane ne wannan Bafiliste, marar kaciya, da zai raina rundunar Allah mai rai?”


Baranka ya taɓa kashe zaki da beyar, wannan arne zai zama kamar ɗaya daga cikinsu, tun da yake ya raina rundunar Allah mai rai.


Ya Allah, har yaushe abokan gābanmu za su yi ta yi mana ba'a? Za su yi ta zargin sunanka har abada ne?


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ