Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 37:19 - Littafi Mai Tsarki

19 suka ƙaƙƙone gumakansu waɗanda ba Allah ba ne ko kaɗan, siffofi ne kurum na itace da na dutse, da mutane suka yi da hannuwansu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

19 Sun jefar da gumakansu cikin wuta suka kuma hallaka su, gama su ba alloli ba ne itace ne kawai da dutse, da hannuwan mutane suka sarrafa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 37:19
25 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ai, mai aikin hannu ne ya yi shi a Isra'ila! Gunki ne ba Allah ba ne. Za a farfashe siffar maraƙin Samariya.


Haka za ku faɗa musu, “Gumakan da ba su yi sammai da duniya ba, za su lalace a duniya da a ƙarƙashin sammai.”


Sauran itacen ya mai da shi gunki. Yana rusunawa ya yi masa sujada. Yana addu'a gare shi yana cewa, “Kai ne Allahna, ka cece ni!”


Dukan waɗannan alloli ba su da amfani, Ba su iya kome ba, ko kaɗan, Gumakansu ba su da ƙarfi, ba su kuma da iko!”


Ku da dukan abin da kuke yi ba kome ba ne, Waɗanda suke yi muku sujada kuwa, Abin ƙyama ne su!


Masassaƙi yakan ce wa maƙerin zinariya, ‘A gaishe ka!’ Wanda yake gyara gumaka ya yi sumul Yana ƙarfafa wanda yake harhaɗa su. Wani yakan ce, ‘Haɗin ya yi kyau,’ Sukan kuma manne gumakan da ƙusoshi.


Yanzu kuwa sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba, Kurwarsu ba za ta tashi ba, Domin ka hukunta su, ka hallaka su. Ba wanda zai ƙara tunawa da su.


Filistiyawa suka gudu, suka bar gumakansu a nan, Dawuda da mutanensa suka kwashe su.


Ya ɗauki siffar ɗan maraƙin da suka yi, ya ƙone ta, ya niƙe, ta zama gari, ya barbaɗa a ruwa, ya sa Isra'ilawa su sha.


Dā da ba ku san Allah ba, kuna bauta wa waɗansu gumaka, waɗanda ga ainihi ba a bakin kome suke ba.


Ƙasarsu tana cike da gumaka, suna sujada ga abubuwan da suka yi da hannuwansu.


Ba za su ƙara dogara ga bagaden da suka yi da hannuwansu ba, ko kuwa su dogara ga ayyukan hannuwansu, ko keɓaɓɓun wuraren da suke wa gumaka sujada, ko bagadai don ƙona turare.


Zan hurta hukuncin da zan yi musu saboda dukan muguntarsu, da suka bar bina, suka ƙona turare ga gumaka, suka kuma bauta wa gumakan da suka yi.


Akwai wata al'umma da ta taɓa sāke gumakanta Ko da yake su ba kome ba ne? Amma mutanena sun sauya darajarsu da abin da ba shi da rai.


Mutum zai iya yi wa kansa alloli? Ai, waɗannan ba alloli ba ne!”


Maimakon haka, sai ka nuna wa Ubangiji girmankai, har ka sa aka kawo maka, kai da fādawanka, da matanka, da ƙwaraƙwaranka, tasoshin Haikalin Ubangiji, kuka sha ruwan inabi a cikinsu. Kuka yabi gumakan zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba su ji, ba su gani, ba su da ganewar kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa.


Zai kwashe gumakansu ganima, da siffofinsu na zubi, ya kai Masar, tare da tasoshinsu na azurfa da na zinariya masu daraja. Zai yi shekaru bai kai wa sarkin arewa yaƙi ba.


Amma Sarkin Assuriya yana da nasa mugayen shirye-shirye da zai yi. Ya yi niyya ya hallaka al'ummai masu yawa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ