Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 33:2 - Littafi Mai Tsarki

2 Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai. Muna sa zuciyarmu gare ka. Ka dinga kiyaye mu yau da gobe, ka kuma cece mu a lokatan wahala.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

2 Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai; muna marmarinka. Ka zama ƙarfinmu kowace safiya, cetonmu a lokacin damuwa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 33:2
35 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ya ga ba wani mutum, ba kuwa wanda zai taimaki waɗanda ake zalunta. Sa'an nan da ikon kansa ya yi nasara, adalcinsa ya goyi bayansa.


Sa'ad da wannan ya faru, kowa zai ce, “Shi Allahnmu ne! Mun dogara gare shi, ya kuwa cece mu. Shi ne Ubangiji. Mun dogara gare shi, yanzu kuwa muna da farin ciki domin ya cece mu!”


Ka taimake mu, mu yaƙi abokan gāba, Domin taimako irin na mutum banza ne!


Ya jama'ata, ku dogara ya Allah a kowane lokaci! Ku faɗa masa dukan wahalarku, Gama shi ne mafakarmu.


Ga Allah kaɗai na dogara, Cetona daga gare shi yake fitowa.


Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, Kullum a shirye yake yă yi taimako a lokacin wahala.


Gari na wayewa sai Musa ya miƙa hannunsa bisa bahar, ruwan kuwa ya koma kamar yadda yake a dā. Da Masarawa suka yi ƙoƙarin tserewa, sai ruwan ya rufe su. Ubangiji kuwa ya hallaka su a tsakiyar bahar.


Ku komo wurin Ubangiji, ku roƙe shi, Ku ce, “Ka gafarta mana zunubanmu, Ka karɓe mu saboda alherinka, Mu kuwa za mu yabe ka da bakinmu.


Su sababbi ne kowace safiya, Amincinka kuma mai girma ne.


Ya kai, wanda kake begen Isra'ila, Mai Cetonta a lokacin wahala, Ƙaƙa ka zama kamar baƙo a ƙasar? Kamar matafiyi wanda ya kafa alfarwarsa a gefen hanya don ya kwana, ya wuce?


Ubangiji yana zuwa ya yi mulki da iko, Zai taho tare da mutanen da ya cece su. Ga shi, zai kawo lada Zai kuma yi wa mutane sakamako.


Ka hukunta jama'arka, ya Ubangiji, A cikin azaba sun yi addu'a gare ka.


Muna bin nufinka, muna sa zuciya gare ka. Kai kaɗai ne bukatarmu.


Matalauta da 'yan ƙaƙa naka yi sun sheƙa zuwa wurinka, Sun sami zaman lafiya a lokatan wahala. Ka ba su mafaka daga hadura, Ka inuwantar da su daga matsanancin zafi. Mugaye sukan tasar musu kamar hadirin ƙanƙara,


Kamar yadda bara yake dogara ga maigidansa, Baranya kuma ga uwargijiyarta, Haka nan muke zuba ido gare ka, ya Ubangiji Allahnmu, Har mu sami jinƙanka.


Sa'ad da suka kira gare ni, zan amsa musu, Zan kasance tare da su sa'ad da suke shan wahala, Zan cece su in girmama su.


Yanzu sai ka sa mu yi farin ciki mai yawa, Kamar yadda ka sa muka yi baƙin ciki A dukan shekarun nan, da muka sha wahala.


Ga Allah kaɗai na dogara, A gare shi na sa zuciyata.


Ku yi kira gare ni sa'ad da wahala ta zo, Zan cece ku, Ku kuwa za ku yabe ni.”


Allah yana zaune cikin birnin, Ba kuwa za a hallaka birnin ba, faufau. Da asuba Allah zai kawo musu gudunmawa.


Ubangiji yakan ceci adalai, Ya kiyaye su a lokatan wahala.


Waɗanda suke dogara gare ka, Ba za su kasa yin nasara ba, Sai dai waɗanda suke gaggawa su yi maka tayarwa.


A gare ka nake dogara, Da safe ka tuna mini da madawwamiyar ƙaunarka. Addu'ata ta hau zuwa gare ka, Ka nuna mini hanyar da zan bi.


Ubangiji ne haskena da cetona, Ba zan ji tsoron kowa ba. Ubangiji yana kiyaye ni daga dukan hatsari, Ba zan ji tsoro ba.


Isra'ila, kin manta da Allah wanda ya kuɓutar da ke, wanda ya kāre ki kamar babban dutse. Kin dasa wa kanki lambuna masu ni'ima don ki yi wa gumaka sujada.


Ga saƙon da ya aike su su faɗa wa Ishaya, “Yau rana ce ta wahala, muna shan hukunci da wulakanci. Mun zama daidai da mace wadda take naƙuda, amma ba ta da ƙarfin da za ta haihu.


Zan zo da sauri in cece su, Lokacina na nasara ya yi kusa. Ni kaina zan yi mulki a kan al'ummai. Manisantan ƙasashe za su jira ni in zo, Za su jira da sa zuciya, ni in cece su.


Ka sa madawwamiyar ƙaunarka ta kasance tare da mu, ya Ubangiji, Da yake a gare ka muke sa zuciya.


Ubangiji ya ɓoye kansa daga jama'arsa, amma ni na dogara gare shi, na kafa zuciyata a gare shi.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ