Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 32:14 - Littafi Mai Tsarki

14 Har ma za a bar fādar, babban birnin sarauta kuma za a gudu a bar shi gaba ɗaya. Gidaje kuma da kagaran da take tsaronsu za su zama rusassu har abada. A can jakunan jeji za su yi ta zarya, tumaki kuma za su sami wurin kiwo.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

14 Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 32:14
27 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Birni mai garu ya zama kufai. An bar shi kamar jejin da ba kowa ciki. Ya zama wurin kiwon shanu, inda za su huta su yi kiwo.


Ka mai da birane kufai Ka lalatar da kagaransu, Wuraren da maƙiya suka gina kuwa, An shafe su har abada.


Birnin ya zama kango, an farfashe ƙofofinsa.


A cikin birni kome ya birkice, an kulle kowane gida don a hana mutane shiga.


Za a kashe waɗansu da kaifin takobi, a kuma kakkama waɗansu a kai su bauta zuwa ƙasashen al'ummai duka. Al'ummai kuma za su tattake Urushalima, har ya zuwa cikar zamaninsu.”


“Sa'ad da kuka ga rundunonin yaƙi sun kewaye Urushalima, sa'an nan ku tabbata ana kusan ribɗe ta.


Na yi tambaya na ce, “Har yaushe zai ta zama haka, ya Ubangiji?” Sai ya amsa, ya ce, “Har birane suka zama kufai ba kowa ciki. Har gidaje suka zama kangwaye. Har ƙasar kanta ta zama ba kowa, marar amfani.


Na ji Ubangiji Mai Runduna yana cewa, “Duk waɗannan manya manyan gidaje kyawawa za su zama kangwaye.


Su ne suke shayar da namomin jeji, Jakunan jeji kuma, a nan sukan kashe ƙishinsu.


Ya ƙone Haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan gidajen urushalima. Ya ƙone kowane babban gida.


“A lokacin nan, waɗannan kyawawan gonakin inabi waɗanda suke da kurangar inabi dubu, kuɗin kowace gonar inabi azurfa dubu guda ne, gonakin za su cika da ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya.


Birnin duka ya ruguntsume, cike da hayaniya da tashin hankali. Mutanenku da suka mutu ba su mutu suna yaƙi ba.


Mu tashi mu fāɗa mata da dare, Mu lalatar da fādodinta.’ ”


Jakunan jeji suna tsaye a kan tuddan da ba ciyawa, Suna haki kamar diloli, Idanunsu ba su gani Domin ba abinci.”


Gama haka Ubangiji, Allah na Isra'ila, ya ce, a kan gidajen da suke a wannan birni, da gidajen sarakunan Yahuza, waɗanda aka rurrushe domin a yi wa garukan jigo saboda mahaurai da suka kewaye birni, da kuma saboda yaƙi.


Sarkin Babila kuwa ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat. Haka aka tafi da mutanen Yahuza bautar talala.


In ba haka ba, sai in yi mata tsiraici, In bar ta kamar ran da aka haife ta. In maishe ta kamar jeji, In bar ta kamar busasshiyar ƙasa, In kashe ta da ƙishi.


Gaɓar teku za ta zama ta mutanen Yahuza waɗanda suka ragu, Wurin da za su yi kiwo. Za su kwanta da maraice a gidajen Ashkelon, Gama Ubangiji Allahnsu zai kula da su, Zai kuwa mayar musu da albarkarsu ta dā.


Wannan shi ne birnin da yake da harka, mai zaman lafiya, Wanda yake ce wa kansa, “Ba wani sai ni.” Ga shi, ya zama kufai, Wurin zaman dabbobi! Duk wanda ya wuce ta wurin, Zai yi tsaki, ya kaɗa kai.


Bayan haka sai ya gina garu a bayan garin Dawuda a yammacin Gihon, a kwari har zuwa Ƙofar Kifi, ya kewaye da shi zuwa Ofel, ya gina shi da tsayi sosai. Sa'an nan ya sa sarakunan yaƙi a garuruwa masu garu na Yahuza.


Ma'aikatan Haikali da suke zaune a Ofel suka yi gyare-gyare zuwa wani wuri daura da Ƙofar Ruwa wajen gabas, har zuwa wata doguwar hasumiya.


Ƙofofin birnin za su yi makoki, su yi kuka. Za a kamanta birnin da matar da take zaune a ƙasa tsirara.


Saboda ku kuwa za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za ta zama tsibin kufai, Dutse inda Haikali yake zai zama kurmi.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ