Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 3:11 - Littafi Mai Tsarki

11 Amma mugaye sun shiga uku, za a sāka musu bisa ga abin da suka aikata.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

11 Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 3:11
36 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ga mugaye ba zai tafi daidai ba, kamar inuwa ransu yake. Za su yi mutuwar ƙuruciya domin ba su da tsoron Allah.


Gama Shari'a marar jinƙai ce ga wanda ba ya nuna jinƙai. Amma jinƙai yana rinjayar hukunci.


Madawwamiyar ƙauna, ta Ubangiji ce. Kai kanka, ya Ubangiji, kake sāka wa Kowane mutum bisa ga ayyukansa.


Ka hukunta su saboda abin da suka aikata. Ka hukunta su saboda dukan ayyukansu, Ka ba su abin da ya cancance su!


Jarirai ba za su mutu tun suna jarirai ba, ko wanne zai cika yawan kwanakinsa kafin ya mutu. Waɗanda suke masu shekara ɗari da haihuwa su ne samari. Waɗanda suka mutu kafin wannan lokaci, to, alama ce, ta cewa na hukunta su.


Ubangiji ya ce, “Ba mafaka domin masu zunubi.”


Saboda haka za ku karɓi sakayyarku, ayyukanku za su cuce ku.


Don lalle ne a gabatar da mu duka, a gaban kursiyin shari'a na Almasihu, domin kowa yă sami sakamakon abin da ya yi tun yana tare da wannan jiki, ko mai kyau ne, ko kuma marar kyau.


Wannan ya yi nesa da kai, da ka aikata irin haka, wato da za ka aza mai adalci daidai yake da mugu! Wannan ya yi nesa da kai! Mahukuncin dukan duniya ba zai yi adalci ba?”


sai ka ji ka yi wa bayinka shari'a daga Sama, ka hukunta wa mugun, ka ɗora masa alhakinsa, ka baratar da adalin, ka ba shi sakayyar adalcinsa.


Da cewa na yi zunubi, na shiga uku ke nan a wurinka. Amma sa'ad da na yi abin kirki ba na samun yabo. Ina baƙin ciki ƙwarai, kunya ta rufe ni.


Sakayyar mutum ta rataya ne a kan maganarsa da aikinsa, zai sami abin da ya cancance shi.


Ubangiji ya ce, “Zan kawo masifa a duniya. Zan hukunta dukan mugaye saboda zunubansu. Zan ƙasƙantar da kowane mai girmankai. Zan hukunta kowane mai izgili da mai mugunta.


“Na riga na ƙudura hukuncinsu, shari'ar da aka yanke kuwa an rubuta ta. Ba zan ƙyale abin da suka aikata ba, amma zan sāka musu


saboda zunubansu da zunuban kakanninsu. Gama suka ƙona turare a ɗakunan tsafin arna na kan tuddai, suka kuwa faɗi mugun abu a kaina. Saboda haka zan hukunta su yadda ya cancance su.”


Zan hukunta ku bisa ga ayyukanku,’ in ji Ubangiji, ‘Zan sa wa jejin ƙasar wuta. Za ta cinye duk abin da yake kewaye da ita.’ ”


Amma kowa zai mutu saboda zunubin kansa, Wanda ya ci inabi masu tsami, Shi ne haƙoransa za su mutu.”


Ya buɗe littafin a gabana, akwai rubutu ciki da baya. Ba abin da aka rubuta sai maganganun baƙin ciki, da makoki, da kaito.


Wanda ya yi zunubi shi zai mutu. Ɗa ba zai ɗauki hakkin laifin mahaifinsa ba, mahaifi kuma ba zai ɗauki hakkin laifin ɗansa ba. Adalcin adali nasa ne, muguntar mugu kuma tasa ce.


Ni, Ubangiji na faɗa, zai tabbata gama zan aikata, ba zan fasa ba, ba kuwa zan ƙyale ba, ba kuma zan bari ba. Zan hukunta ki saboda hanyoyinki da ayyukanki, ni Ubangiji Allah na faɗa.”


Idan na hurta, cewa hakika mugu zai mutu, amma ba ka faɗakar da shi don ya juyo, ya bar muguwar hanyarsa ba, wannan mugun zai mutu saboda laifinsa, amma zan nemi hakkin jininsa a hannunka.


Sa'an nan za su yi kuka ga Ubangiji, Amma Ubangiji ba zai amsa musu ba. Zai ɓoye musu fuskarsa a wannan lokaci, Saboda mugayen ayyukansu.


Duniya kuwa za ta zama kufai, Saboda mazaunan da suke cikinta, Saboda hakkin ayyukansu.


Idan kuwa ba ku yi haka ba, kun yi wa Ubangiji laifi, ku tabbata fa alhakin zunubinku zai kama ku.


Haka kuwa Allah ya sa muguntar mutanen Shekem ta koma kansu. Bakin Yotam, ɗan Yerubba'al, kuma ya kama su.


Yau na raunana, ko da yake ni sarki ne naɗaɗɗe. Waɗannan mutane, 'ya'yan Zeruya, sun fi ƙarfina, Ubangiji ya sāka wa mai aikata mugunta da muguntar da ya aikata.”


Saboda haka Ubangiji ya ce maka, ‘Ga shi, zan kawo maka masifa, in shafe ka, in datse maka kowane ɗa namiji, bawa ko ɗa, a Isra'ila.


Idan an sāka wa mutumin kirki da alheri a duniya, hakika za a hukunta wa mugaye da masu zunubi.


Wanda ya haƙa ramin mugunta shi zai faɗa ciki, wanda kuma ya mirgino dutse, zai fāɗo a kansa.


“Ni Ubangiji Allah na ce, zan yi miki yadda kika yi, ke da kika yi rantsuwar kafara, kika ta da alkawari.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ