Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 29:5 - Littafi Mai Tsarki

5 Ya Urushalima, dukan baƙin da suka auka miki da yaƙi za a hure su kamar yadda iska take hure ƙura, sojojinsu kuma masu firgitarwa za a hure su kamar yadda iska take hure tattaka. Farat ɗaya ba zato ba tsammani,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

5 Amma abokan gābanki masu yawa za su zama kamar ƙura mai laushi, sojojinsu masu firgitarwa za su yi ta tashi kamar yayin da iska ta hura. Farat ɗaya, cikin ɗan lokaci,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 29:5
24 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Lokacin da mutane suke cewa, “Muna zaman salama da zaman lafiya,” wuf; sai halaka ta auko musu, kamar yadda naƙuda take kama mace mai ciki, ba kuwa hanyar tsira.


Mala'ikan Ubangiji kuwa ya shiga sansanin Assuriyawa ya kashe sojoji dubu ɗari da dubu tamanin da dubu biyar (185,000). Da asuba ta yi, sai ga su can kwankwance, duk sun mutu!


Kun yi laifi. Kuna kamar bango wanda ya tsage daga bisa har ƙasa. Za ku fāɗi ba zato ba tsammani.


Assuriya za ta hallaka cikin yaƙi, amma ba ta wurin ikon mutum ba. Assuriyawa za su gudu daga bakin dāga, za a mai da majiya ƙarfinsu bayi.


Masarawa su ba Allah ba ne, mutane ne kurum! Dawakansu ba su wuce ikon ɗan adam ba! Sa'ad da Ubangiji zai matsa, ƙaƙƙarfar al'umma za ta marmashe, al'ummar da aka yi wa taimako kuma za ta fāɗi. Dukansu za su hallaka.


Kamar fari a ƙeƙasasshiyar ƙasa. Amma kai, ya Ubangiji, ka rufe bakin abokan gābanmu, Ka sa hayaniyar mugaye ta yi tsit, Kamar yadda girgije yake sanyaya zafin rana.


Ka sa su zama kamar tattakar da iska take kwashewa, Kamar waɗanda mala'ikan Ubangiji yake korarsu!


Amma mugaye ba haka suke ba, Su kamar yayi suke wanda iska take kwashewa.


Ya kuma sa su zama kamar tattakar da iska yake kwashewa? Ko kuma kamar ƙura wadda hadiri yake kwashewa?


Ubangiji ya ce, “Zan kawo masifa a duniya. Zan hukunta dukan mugaye saboda zunubansu. Zan ƙasƙantar da kowane mai girmankai. Zan hukunta kowane mai izgili da mai mugunta.


Jama'ar al'ummai masu iko za su yabe ka, Za a ji tsoronka a biranen mugayen al'ummai.


Matalauta da 'yan ƙaƙa naka yi sun sheƙa zuwa wurinka, Sun sami zaman lafiya a lokatan wahala. Ka ba su mafaka daga hadura, Ka inuwantar da su daga matsanancin zafi. Mugaye sukan tasar musu kamar hadirin ƙanƙara,


Zai zama ƙarshen waɗanda suke zaluntar waɗansu, suna raina Allah. Za a hallakar da kowane mai zunubi.


Al'ummai ba kome ba ne a wurin Ubangiji, Ba su fi ɗigon ruwa ba, Manisantan tsibirai ba su fi ƙura nauyi ba.


“Su waɗanda suke fushi da ku, ku jama'ata, Za a ƙasƙantar da su su ji kunya. Waɗanda suke faɗa da ku kuwa za su mutu.


Zan sa ku zama kamar abin sussuka, Wanda yake sabo, mai kaushi, mai tsini. Za ku sussuke duwatsu ku lalatar da su, Za a marmashe tuddai kamar ƙura.


Za ku watsa su sama cikin iska, Iska za ta hure su, ta tafi da su, Hadiri kuma zai warwatsar da su. Amma za ku yi murna, gama ni ne Allahnku, Za ku yabe ni, Allah Mai Tsarki na Isra'ila.


Duk da haka bala'i zai auko miki, Ba ɗaya daga cikin sihirinki da zai tsai da shi ba, Lalacewa za ta auko a kanki farat ɗaya, Lalacewar da ba ki taɓa ko mafarkinta ba!


Ubangiji ya ce wa Isra'ila, “Tuntuni na yi faɗi a kan abin da zai faru, Sa'an nan na sa ya faru ba labari!


Ya kawo halaka a kan ƙarfafa, Da a kan birane masu garu.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ