Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 25:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Ya Ubangiji, kai ne Allahna, Zan ɗaukaka ka, in yabi sunanka. Ka aikata al'amura masu banmamaki, Ka tafiyar da su da aminci, Wato bisa ga shirin da ka yi tuntuni.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 25:1
41 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, Shi ne wanda ya cece ni. Wannan ne Allahna, zan yabe shi, Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.


Kai ne Allahna, kai nake yi wa godiya, Zan yi shelar girmanka.


Allah ba kamar mutum ba ne, da zai yi ƙarya, Ba kuwa ɗan mutum ba ne, da zai tuba. Zai cika dukan abin da ya alkawarta, Ya hurta, ya kuwa cika.


Ku raira sabuwar waƙa ga Ubangiji, Gama ya aikata ayyuka masu banmamaki! Ta wurin ikonsa, da ƙarfinsa mai tsarki ya yi nasara.


Urushalima tana murna saboda abin da Ubangiji ya yi. Tana kama da amaryar da ta sha ado a ranar aurenta. Allah ya suturce ta da ceto da nasara.


Dukan wannan hikima daga wurin Ubangiji Mai Runduna ne. Shirye-shiryen da Allah ya yi na hikima ne kullum kuwa sukan yi nasara!


Ka yi mana abubuwa masu yawa, ya Ubangiji Allahna. Ba wani kamarka! Idan na yi ƙoƙari in faɗe su duka, Sun fi ƙarfin in faɗa.


A cikinsa ne aka maishe mu abin gādo na Allah, an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukkan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi,


Ya ce, “Ku yi shiru, ku sani ni ne Allah, Maɗaukaki ne cikin sauran al'umma, Maɗaukaki kuma a duniya!”


Sai na ga sama ta dāre, sai ga wani farin doki! Mahayinsa kuwa ana ce da shi Amintacce, Mai Gaskiya, yana hukunci da adalci, yana kuma yaƙi.


Tun da farko na faɗa muku yadda abin zai zama, Tuntuni na yi faɗi a kan abin da zai faru. Na kuwa ce shirye-shiryena ba za su taɓa fāɗuwa ba, Zan aikata dukan abin da na yi niyyar yi.


suna cewa, “Hakika! Yabo, da ɗaukaka, da hikima, da godiya, da girma, da iko, da ƙarfi su tabbata ga Allahnmu har abada abadin! Amin! Amin!”


Ya Ubangiji Allahnmu, waɗansu sun mallake mu, Amma kai kaɗai ne Ubangijinmu.


Zan yabe shi muddin raina. Zan raira waƙa ga Allahna dukan kwanakina.


Ku yabi Ubangiji Allahnmu, Ku yi sujada a gaban kursiyinsa! Mai Tsarki ne shi!


Suna raira waƙar da Musa bawan Allah ya yi, da kuma wadda ake yi wa Ɗan Ragon nan, suna cewa, “Ayyukanka manya ne, masu banmamaki, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki! Hanyoyinka na adalci ne, na gaskiya ne kuma, Ya Sarkin al'ummai.


Ba za mu ɓoye waɗannan abubuwa daga 'ya'yanmu ba, Amma za mu faɗa wa tsara mai zuwa Labarin ikon Ubangiji, da manya manyan ayyukansa, Da abubuwan banmamaki waɗanda ya aikata.


Zan yi shelar girmanka, ya Allahna, Sarkina, Zan yi maka godiya har abada abadin.


Ubangiji ba zai bar mu mu manta da ayyukansa masu banmamaki ba, Shi mai alheri ne, mai jinƙai kuma.


Ya Ubangiji zan raira waƙar Madawwamiyar ƙaunarka koyaushe, Zan yi shelar amincinka a dukan lokaci.


Ga amsar da Ishaya ya ba Ahaz, “Kasa kunne yanzu, kai zuriyar sarki Dawuda. Ba abin kirki kuke yi ba, da kuka ƙure haƙurin jama'a, haƙurin Allah kuma kuke so ku ƙure?


Zai yi mulkin mutanensa da adalci da mutunci.


Rana tana zuwa sa'ad da jama'a za su raira waƙa, su ce, “Ina yabonka ya Ubangiji! A dā ka yi fushi da ni, Amma yanzu kana yi mini ta'aziyya, ba za ka ƙara yin fushi da ni ba.


Muna bin nufinka, muna sa zuciya gare ka. Kai kaɗai ne bukatarmu.


Isra'ila, me ya sa kake gunaguni, Cewa Ubangiji bai san wahalarka ba, Ko ya kula ya daidaita abubuwa dominka?


Na ce, “Na yi aiki, amma a banza ne. Na mori ƙarfina, amma ban ƙulla kome ba.” Duk da haka na dogara ga Ubangiji, ya daidaita al'amura, Shi zai sāka mini abin da na yi.


Ubangiji ya zaɓe ni tun kafin a haife ni. Ya maishe ni bawansa domin in komo da mutanensa, In komo da jama'ar Isra'ilan da aka warwatsar. Ubangiji ya ba ni daraja, Shi ne tushen ƙarfina.


Yanzu za ku ci abinci a wadace ku ƙoshi, Za ku yabi sunan Ubangiji Allahnku, Wanda ya yi muku abubuwa masu banmamaki, Ba kuma za a ƙara kunyatar da mutanena ba.


Kana lura da ni kullum, Ka cece ni daga magabtana, Daga waɗanda suke tsananta mini.


Ba ka bukatar baye-baye da hadayu, Ba ka so a miƙa maka hadayun ƙonawa Na dabbobi a bisa bagade ba, Ko baya-baye don a kawar da zunubai. A maimakon haka, ka ba ni kunnuwan da zan saurare ka.


“Na ƙayyade lokacin yin shari'a,” in ji Ubangiji Allah, “Zan kuwa yi shari'ar gaskiya.


Ina kiran wani mutum ya zo daga gabas, Zai kawo sura kamar shaho, Zai kammala abin da na shirya. Na yi faɗi, zai kuwa cika.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ