Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 21:2 - Littafi Mai Tsarki

2 Na ga wahayi na waɗansu mugayen abubuwa, wato na cin amana da hallakarwa. Rundunar sojojin Elam, ku kama yaƙi! Rundunar sojojin Mediya ku kewaye birane da yaƙi. Allah zai kawar da wahalar da Babila ta haddasa.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 21:2
44 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Maganar da Ubangiji ya yi wa annabi Irmiya a kan Elam a farkon sarautar Zadakiya Sarkin Yahuza.


Magabtanmu sun shiga uku! Sun yi fashi sun ci amana, ko da yake ba wanda ya yi musu fashi ko cin amana. Amma lokacinsu na fashi da na cin amana zai ƙare, su ne kuma za a yi wa fashi da cin amana.


Daga manisantan wurare na duniya za mu ji waƙoƙin yabon Isra'ila, al'umma adala. Amma ba ni da sauran sa zuciya! Lalacewa nake yi! Maciya amana suna ta cin amana, cin amanarsu sai gaba gaba yake yi.


Ka sa jama'arka su sha wahala ƙwarai, Ka ba mu ruwan inabin da ya bugar da mu.


Kowa aka ƙaddara wa bauta, sai ya je aikin bautar. Kowa kuwa ya yi kisa da takobi, to, kuwa da takobi za a kashe shi lalle. Wannan yana nuna jimiri da bangaskiya na tsarkaka.


Ma'anar PERES ita ce an raba mulkinka, an ba mutanen Mediya da na Farisa.”


“Ragon nan mai ƙaho biyu da ka gani, sarakunan Mediya ne da na Farisa.


“Ka sa mugayen ayyukansu su bayyana a gabanka, Sa'an nan ka hukunta su kamar yadda ka hukunta ni saboda dukan laifofina. Gama nishe-nishena sun yi yawa. Zuciyata kuma ta karai.”


Ko da Babila za ta hau samaniya, Ta gina kagara mai ƙarfi a can, Duk da haka zan aiki masu hallakarwa a kanta, Ni Ubangiji na faɗa.”


Zan hukunta Bel, gunkin Babila, Zan sa ya yi aman abin da ya haɗiye, Ƙasashen duniya ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Garun Babila ya rushe!”


Ku wasa kibau, ku cika kwaruruwanku! Ubangiji ya ta da ruhun sarakunan Mediyawa, Domin yana niyyar hallaka Babila. Gama Ubangiji zai yi ramuwa saboda Haikalinsa.


Mai fansarsu mai ƙarfi ne, Ubangiji Mai Runduna ne sunansa. Hakika zai tsaya musu don ya kawo wa duniya salama, Amma zai kawo wa mazaunan Babila fitina.


“Dukanku 'yan baka, ku ja dāga, ku kewaye Babila, Ku harbe ta, kada ku rage kibanku, Gama ta yi wa Ubangiji zunubi.


kai ka ce, ‘Kaitona, gama Ubangiji ya ƙara baƙin ciki a kan wahalaina, na gaji da nishina, ba ni da hutu!’


Gama zan biya bukatar waɗanda suka gaji, in wartsakar da waɗanda ransu ya yi yaushi.”


Ashe, Ifraimu ba ƙaunataccen ɗana ba ne? Ashe, shi ba ɗan gaban goshina ba ne? A duk lokacin da na ambace shi a kan muguntarsa Nakan tuna da shi da ƙauna. Saboda na ƙwallafa zuciyata a kansa, Hakika zan yi masa jinƙai, ni Ubangiji na faɗa.


Na yi fushi da mutanena, Na maishe su kamar su ba nawa ba ne. Na sa su a ƙarƙashin ikonki, Ba ki kuwa yi musu jinƙai ba, Har da tsofaffi ma kin ba su wuya.


Za su kai Urushalima da murna, Suna raira waƙa suna sowa don murna. Za su yi farin ciki har abada, Ba damuwa da ɓacin rai har abada.


Sojojin ƙasar Elam sun zo kan dawakai suna rataye da kwari da baka. Sojojin ƙasar Kir sun shirya garkuwoyinsu.


Basira takan sa a girmama ka, amma mutanen da ba za a iya amincewa da su ba, a kan hanyar hallaka suke.


Ka kasa kunne ga nishin 'yan sarƙa, Ka kuɓutar da waɗanda aka yanke musu hukuncin kisa, Ta wurin ikonka mai girma.


Ubangiji ya ce, “Amma zan zo yanzu, Domin ana zaluntar masu bukata, Waɗanda aka tsananta musu kuma, suna nishi don zafi. Zan ba su zaman lafiya da suke nema!”


Mutanen dā suna da karin magana cewa, ‘Daga cikin masu mugunta take fitowa.’ Hannuna dai ba zai taɓa ka ba.


A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, Sarkin Assuriya ya ci Samariya, ya kwashe Isra'ilawa zuwa Assuriya, ya ajiye su a Hala, da Habor a bakin kogin Gozan, da cikin garuruwan Mediyawa.


Waɗanda suke dogara gare ka, Ba za su kasa yin nasara ba, Sai dai waɗanda suke gaggawa su yi maka tayarwa.


Sa'ad da na dubi waɗannan maciya amana, Sai in ji ƙyama ƙwarai, Domin ba su yi biyayya da umarninka ba.


Belshazzar sarki fa ya firgita ƙwarai, fuskarsa ta turɓune, fādawansa duk suka ruɗe.


'Ya'yan Shem su ne Elam, da Asshur, da Arfakshad, da Lud, da Aram.


A wannan rana Ubangiji zai sāke zuwa, ya nuna ikonsa. Zai komo da mutanensa gida waɗanda suka ragu a Assuriya, da Masar, da ƙasashen Fatros, da Habasha, da Elam, da Babila, da Hamat, da kuma ƙasashen bakin gāɓa da na tsibiran teku.


Sa'ad da ya aikata wannan za su yi wa Sarkin Babila ba'a. Za su ce, “Mugun sarkin ya fāɗi, ba zai ƙara zaluntar kowa ba!


Yanzu magana ta ƙare, duniya duka tana jin daɗin hutawa da salama. Kowa na ta raira waƙar murna.


Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Zan karya bakan Elam, inda ƙarfinta yake.


A wahayin sai na gani ina a bakin kogin Ulai a Shushan, masarautar lardin Elam.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ