Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 2:22 - Littafi Mai Tsarki

22 Kada ku dogara ga 'yan adam. Wace daraja take gare su?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

22 Ku daina dogara ga mutum, wanda numfashi ne kawai yake da shi a hancinsa. Wace daraja gare shi?

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 2:22
14 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ubangiji ya ce, “La'ananne ne mutumin da yake dogara ga mutum, Wanda jiki ne makaminsa, Wanda ya juya wa Ubangiji baya,


Kada ka dogara ga shugabanni, Ko kowane mutum da ba zai iya cetonka ba.


Alhali kuwa ba ku san abin da gobe za ta kawo ba. Wane iri ne ranku? Ai, kamar hazo yake, jim kaɗan sai ya ɓace.


Wane ne mutum, har da kake tunawa da shi, Mutum kurum, har da kake lura da shi?


Al'ummai ba kome ba ne a wurin Ubangiji, Ba su fi ɗigon ruwa ba, Manisantan tsibirai ba su fi ƙura nauyi ba.


Talakawa kamar shaƙar numfashi suke, Manyan mutane, su ma haka suke marasa amfani. Ko an auna su a ma'auni, sam ba su da nauyin kome, Sun fi numfashi shakaf.


da kowane abin da yake bisa sandararriyar ƙasa wanda yake da numfashin rai cikin kafafen hancinsa ya mutu.


Sa'an nan Ubangiji Allah ya siffata mutum daga turɓayar ƙasa, a cikin kafafen hancinsa kuwa ya hura numfashin rai, mutum kuma ya zama rayayyen taliki.


Muddin ina numfashi, Ruhun Allah kuma yana cikin hancina


Al'ummai ba kome ba ne ko kaɗan a gare shi.


Ubangiji ya ce, “Ni ne wanda yake ƙarfafa ku. Don me za ku ji tsoron mutum mai mutuwa, Wanda bai fi ciyawa tsawon rai ba?


A ganinmu masu girmankai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suke yi ba, amma sukan jarraba Allah da mugayen ayyukansu su kuwa zauna lafiya.’ ”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ