Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 16:14 - Littafi Mai Tsarki

14 Yanzu Ubangiji ya ce, “A shekara uku daidai, dukiyar Mowab mai yawan nan za ta ƙare. Daga cikin ɗumbun mutanenta 'yan kaɗan ne kaɗai za su ragu, za su kuma zama marasa ƙarfi.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

14 Amma yanzu Ubangiji ya ce, “Cikin shekara uku, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, haka za a mai da daraja da kuma dukan yawan mutanen Mowab abin reni, daga ɗumbun mutanenta, ’yan kaɗan ne kaɗai za su ragu, za su kuma zama marasa ƙarfi.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 16:14
18 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Za a hallaka Mowab daga zaman al'umma, Domin ta tayar wa Ubangiji.


Ubangiji Mai Runduna ne ya shirya wannan! Ya shirya haka ne don ya kawo ƙarshen girmankanta saboda abin da suka aikata, don ya ƙasƙantar da manyan mutanenta.


Sa'an nan Ubangiji ya ce mini, “Saura shekara ɗaya tak girman kabilar Kedar zai ƙare.


Ubangiji ya ce, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa, kada mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa, kada kuma mawadaci ya yi fariya da wadatarsa.


Ubangiji zai kiyaye Dutsen Sihiyona, amma za a tattake jama'ar Mowab a ƙasa, kamar yadda ake tattake tattaka cikin taki.


Ubangiji ya ce, “Rana taba zuwa, ran da girman Isra'ila zai ƙāre, fatara za ta gāje gurbin dukiyarsu.


Zuciyata ta yi kuka ainun saboda Mowab! Mutane sun gudu zuwa cikin garin Zowar. Waɗansu sun haura zuwa Luhit, suna tafe suna kuka, waɗansu sun tsere zuwa Horonayim, suna hargowa saboda baƙin ciki.


Kafin lokacin ya yi, ƙasashen sarakunan nan biyu waɗanda suka firgita ku za su zama kango.


Ya faɗa musu darajar wadatarsa, da yawan 'ya'yansa, da yawan matsayin da sarki ya girmama shi da su, da yadda sarki ya ciyar da shi gaba fiye da sarakuna da barorin sarki.


Amma ku ba shi hannu sake, ku ranta masa abin da yake so gwargwadon bukatarsa.


Yakubu ya ji 'ya'yan Laban suna cewa, “Yakubu ya kwashe dukan abin da yake na mahaifinmu, daga cikin dukan abin da yake na mahaifinmu kuma ya sami dukiyarsa.”


“Kamar kamen soja na tilas, Haka zaman 'yan adam take, Kamar zaman mai aikin bauta.


Ka kawar da fuska daga gare shi, ka rabu da shi, Ka bar shi ya ji daɗin kwanakinsa na fama da aiki idan zai iya.


Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma, su washe mutanen da suke wajen gabas. Za su ci nasara a kan mutanen Edom da na Mowab, jama'ar Ammon kuwa za su yi musu biyayya.


Wannan shi ne jawabin da Ubangiji ya riga ya yi a kan Mowab.


Za su miƙa hannuwansu kamar suna ƙoƙarin yin ninƙaya, amma girmankansu zai jā hannuwansu ƙasa a duk sa'ad da suka ɗaga.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ