Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 13:21 - Littafi Mai Tsarki

21 Za ta zama wurin zaman namomin jejin hamada, inda mujiyoyi za su yi sheƙarsu. Jiminai za su zauna a can, awakin jeji za su yi ta warnuwa a cikin kufanta.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

21 Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 13:21
10 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Sai ya yi kira da murya mai ƙarfi, ya ce, “Ta fāɗi! Babila mai girma ta fāɗi! Ta zama mazaunin aljannu, Matattarar kowane baƙin aljani, Da kowane irin ƙazamin tsuntsu, abin ƙyama.


(Mutanen Babila ne, ba na Assuriya ba, waɗanda suka bar namomin jeji su murƙushe Taya. Mutanen Babila ne suka gina hasumiya, suka ragargaza kagarar Taya suka bar birnin kango.)


Har ma za a bar fādar, babban birnin sarauta kuma za a gudu a bar shi gaba ɗaya. Gidaje kuma da kagaran da take tsaronsu za su zama rusassu har abada. A can jakunan jeji za su yi ta zarya, tumaki kuma za su sami wurin kiwo.


“Domin haka namomin jeji da diloli za su zauna a Babila, Haka kuma jiminai. Ba za a ƙara samun mazauna a cikinta ba har dukan zamanai.


Mika ya ce, “Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka, Zan tuɓe, in yi tafiya huntu. Zan yi kuka kamar diloli, In yi baƙin ciki kamar jiminai.


Tumaki za su kwanta a tsakiyarta, Da kuma kowace irin dabba ta kowace ƙasa. Mujiya da bushiya za su zauna a kan ginshiƙanta, Ga muryar kuka a taga. Ga risɓewa a bakin ƙofa, Gama za a kware rufin katakan itacen al'ul.


Zan su Babila ta zama fadama, mujiyoyi za su zauna a can. Zan kuwa share Babila da tsintsiyar da za ta share kome. Ni, Ubangiji Mai Runduna, na faɗa.”


Ka mai da birane kufai Ka lalatar da kagaransu, Wuraren da maƙiya suka gina kuwa, An shafe su har abada.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ