Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Ishaya 12:4 - Littafi Mai Tsarki

4 A wannan rana jama'a za su raira waƙa, su ce, “Ku yi wa Ubangiji godiya! Ku nemi taimako a gare shi! Ku faɗa wa dukan sauran al'umma abin da ya aikata! Ku faɗa musu irin girman da yake da shi!

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

4 A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Ishaya 12:4
42 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar girmansa, Ku sanar wa sauran al'umma abubuwan da ya yi!


Girma, da iko, da daraja, da nasara, da ɗaukaka duk naka ne, ya Ubangiji, gama dukan abin da yake cikin sammai da duniya naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji. Kai ne Maɗaukaki duka.


Ya Ubangiji, kai ne Allahna, Zan ɗaukaka ka, in yabi sunanka. Ka aikata al'amura masu banmamaki, Ka tafiyar da su da aminci, Wato bisa ga shirin da ka yi tuntuni.


Na sanar da su sunanka, zan kuma sana, domin ƙaunar da ka yi mini tă kasance cikinsu, ni ma in kasance a cikinsu.”


“Ku ba da labari ga sauran al'umma, ku yi shela, Ku ta da tuta, ku yi shela, Kada ku ɓuya, amma ku ce, ‘An ci Babila da yaƙi, An kunyatar da Bel, An kunyatar da siffofinta, Merodak ya rushe, Gumakanta kuma sun ragargaje!’


Ka bayyana girmanka ya Allah, a sararin sama, Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!


Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga mai kāre ni! Allah ne, Mai Cetona! A yi shelar girmansa!


Waɗannan Lawiyawa kuma, wato Yeshuwa, da Kadmiyel, da Bani, da Hashabnaiya, da Sherebiya, da Hodiya, da Shebaniya, da Fetahiya su ne suka yi kiran sujada, suka ce, “Ku miƙe tsaye, ku yabi Ubangiji Allahnku, Ku yabe shi har abada abadin. Bari kowa ya yabi maɗaukakin sunanka, ya Ubangijii, Ko da yake ba yabon da ɗan adam zai yi har ya isa.”


Sai Ubangiji ya ce masa, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka, zan kuma yi alheri ga wanda nā yi wa alheri, in nuna jinƙai ga wanda nā yi wa jinƙai.”


Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, Shi ne wanda ya cece ni. Wannan ne Allahna, zan yabe shi, Allah na kakana, zan ɗaukaka shi.


su kuwa sani ni ne wanda yake hukunta musu. “Amma zan bar waɗansu, in aika da su ga al'ummai da manisantan ƙasashe inda ba a ji labarin sunan da na yi ba, ba a kuwa ga girmana da ikona ba, wato zuwa Tarshish, da Libiya, da Lidiya, duk da gwanayen maharbanta, Rosh da Tubal, da kuma Helas. Za su ba da labarin girmana ga waɗannan al'ummai.


Ubangiji da girma yake! Yana mulki a kan kome. Zai cika Urushalima da adalci da mutunci,


waɗanda suke wajen gabas kuma za su yabe shi. Jama'ar da take zaune a gefen teku za su yabi Ubangiji, Allah na Isra'ila.


Rana tana zuwa sa'ad da jama'a za su raira waƙa, su ce, “Ina yabonka ya Ubangiji! A dā ka yi fushi da ni, Amma yanzu kana yi mini ta'aziyya, ba za ka ƙara yin fushi da ni ba.


Girmankan ɗan adam zai ƙare, za a hallakar da fāriyar ɗan adam, Ubangiji ne kaɗai za a ɗaukaka sa'ad da wannan rana ta yi,


Rana tana zuwa sa'ad da girmankan 'yan adam zai ƙare, zai kuma lalatar da fāriyar 'yan adam. Sa'an nan Ubangiji ne kaɗai za a ɗaukaka.


Ba wani kamar Ubangiji Allahnmu. Yana zaune a can ƙwanƙolin sama,


Dole su gode masa, su miƙa masa hadayu, Su raira waƙoƙin murna, Su faɗi dukan abin da ya yi!


Ya Ubangiji Mai Iko Dukka, kai kake mulkin dukan duniya, Ka fi sauran alloli duka girma.


Ku yi shelar ɗaukakar Ubangiji ga sauran al'umma, Ku yi shelar ayyukansa masu girma ga dukan kabilai.


Amma a gare ni, ya fi mini kyau, in kasance kusa da Allah! Na sami mafaka a wurin Ubangiji Allah, Da zan yi shelar dukan abin da ya aikata.


Ya ce, “Ku yi shiru, ku sani ni ne Allah, Maɗaukaki ne cikin sauran al'umma, Maɗaukaki kuma a duniya!”


Ka yi mana abubuwa masu yawa, ya Ubangiji Allahna. Ba wani kamarka! Idan na yi ƙoƙari in faɗe su duka, Sun fi ƙarfin in faɗa.


Ku yi shelar girman Ubangiji tare da ni, Mu yabi sunansa tare!


Mutanen da ba a haifa ba tukuna, za a faɗa musu, “Ubangiji ya ceci jama'arsa!”


Ya Ubangiji, ka zo da ƙarfinka! Za mu raira waƙa mu yabi ikonka.


Ku yabi Ubangiji, shi da yake mulki a Sihiyona! Ku faɗa wa kowace al'umma abin da ya yi!


Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar girmansa, Ku sanar wa sauran al'umma abubuwan da ya yi!


Bari dukansu su yabi sunan Ubangiji, Sunansa ya fi dukan sauran sunaye girma, Ɗaukakarsa kuwa tana bisa duniya da samaniya!


Muna bin nufinka, muna sa zuciya gare ka. Kai kaɗai ne bukatarmu.


Bari waɗanda suke a manisantan ƙasashe su yi yabo, Su kuma girmama Ubangiji!


Ku fita daga Babila, ku tafi a sake! Ku yi sowar albishir da farin ciki, ku sa a sani a ko'ina, “Ubangiji ya fanshi bawansa Isra'ila!”


“Mutane daga kowaɗanne sassa na duniya za su girmama ni. Ko'ina za su ƙona mini halattacciyar hadaya, gama dukansu za su girmama ni,” in ji Ubangiji Mai Runduna.


Allah, wanda yake zaune a tsattsarkan Haikalinsa, Yana lura da marayu, yana kuwa kiyaye gwauraye, Wato matan da mazansu suka mutu.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ