Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 9:21 - Littafi Mai Tsarki

21 Gama mutuwa ta shiga tagoginmu, Ta shiga cikin fādodinmu, Ta karkashe yara a tituna, Ta kuma karkashe samari a dandali.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

21 Mutuwa ta haura ta tagoginmu ta kuma shiga katangarmu; ta karkashe ’ya’ya a tituna ta kuma karkashe samari a dandali.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 9:21
17 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Don haka ina cike da fushin Ubangiji Na gaji da kannewa. Ubangiji ya ce, “Zan kwararo fushi kan yara da suke a titi. Da kuma kan tattaruwar samari. Za a ɗauke mata da miji duka biyu, Da tsofaffi, da waɗanda suka tsufa tukub-tukub. Za a ba waɗansu gidajensu, da gonakinsu, da matansu, Gama zan nuna ikona in hukunta mazaunan ƙasar.


Na sheƙe su da abin sheƙewa a ƙofofin garuruwan ƙasar. Na sa 'ya'yansu su mutu, na hallaka mutanena, Ba su daina yin mugayen ayyukansu ba.


Don haka Ubangiji ya bashe su ga Sarkin Kaldiyawa wanda ya karkashe samarinsu da takobi a Haikali, bai yi juyayin saurayi, ko budurwa, ko tsoho, ko gajiyayye ba. Allah ya bashe su duka a hannunsa.


Har da waɗanda suke yara ma, sukan ji kasala, Samari sukan siƙe su fāɗi,


Don haka, ni Ubangiji na ce, Zan sa abin tuntuɓe a gaban wannan jama'a, Za su kuwa yi tuntuɓe, su fāɗi. Iyaye tare da 'ya'yansu, da maƙwabci, Do abokansu za su lalace.”


Saboda haka ka kawo wa 'ya'yansu yunwa, Ka bashe su ga takobi, Bari matansu su rasa 'ya'ya, mazansu su mutu, Ka sa annoba ta kashe mazansu, A kashe samarinsu da takobi a yaƙi.


“Yanzu, ni Ubangiji Allah Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ina tambaya, me ya sa kuke jawo wa kanku wannan babbar masifa, kuna so ku hallakar da mata da maza, yara da jarirai daga cikin Yahuza, har a rasa wanda zai wanzu?


Domin haka samarinta za su fāɗi a tituna. Za a hallaka sojojinta duka a wannan rana, Ni Ubangiji na faɗa.


Takan ruga cikin birni, Takan hau garu a guje, Takan hau gidaje, Takan shiga ta tagogi kamar ɓarawo.


Ko da a ce mutum goma ne suka ragu a gida guda, duk za su mutu.


Gawawwakin mutanen nan za su zama abincin tsuntsaye da na namomin jeji, ba wanda zai kore su.


Za a shimfiɗa su a rana, da a farin wata, da a gaban dukan rundunan sama, waɗanda suka ƙaunata, suka bauta wa, waɗanda suka nemi shawararsu, suka yi musu sujada. Ba za a tattara su a binne ba, amma za su zama juji a bisa ƙasa.


Isra'ila ta fāɗi, Ba kuwa za ta ƙara tashi ba. Tana fa kwance a ƙasa, Ba wanda zai tashe ta.


“Zan aukar wa mutane da wahala, Za su kuwa yi tafiya kamar makafi, Domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura, Namansu kuwa kamar taroso.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ