Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 7:33 - Littafi Mai Tsarki

33 Gawawwakin mutanen nan za su zama abincin tsuntsaye da na namomin jeji, ba wanda zai kore su.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

33 Sa’an nan gawawwakin wannan mutane za su zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namun jeji, ba za a kuwa sami wani da zai kore su ba.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 7:33
19 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ashe, abin gadon nan nawa ya zama dabbare-dabbaren tsuntsun nan ne mai cin nama? Tsuntsaye masu cin nama sun kewaye shi? Tafi, ka tattaro namomin jeji, Ka kawo su su ci.


Gawawwakinku za su zama abinci ga dukan tsuntsayen sama, da namomin duniya. Ba wanda zai kore su.


Za ka fāɗi matacce a kan duwatsun Isra'ila, kai da dukan rundunanka, da jama'ar da suke tare da kai. Zan ba da gawawwakinka ga tsuntsaye da dabbobi masu cin nama.


zan bashe su a hannun abokan gabansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsaye da namomin jeji.


Waɗanda Ubangiji ya kashe a wannan rana, Za su zama daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Ba za a yi makoki dominsu ba, Ba kuwa za a tattara gawawwakinsu a binne ba. Za su zama taki ga ƙasa.


Za a binne shi kamar jaki, Za a ja shi a yar a bayan ƙofofin Urushalima.”


A wannan wuri zan wofinta dabarun Yahuza da na Urushalima, zan sa a kashe jama'arsu da takobi, a gaban abokan gābansu, ta hannun waɗanda suke neman ransu. Zan ba da gawawwakinsu su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namomin jeji.


za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi makoki dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba. Za su zama juji. Takobi da yunwa za su kashe su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namomin jeji.”


Ubangiji ya ce mini, ‘Ka yi magana, cewa gawawwakin mutane za su fāɗi tuli Kamar juji a saura, Kamar dammunan da masu girbi suka ɗaura, Ba wanda zai tattara su.’ ”


Za a bar gawawwakin sojojinsu a fili domin tsuntsaye da namomin jeji su zama abincin tsuntsaye da bazara, abincin namomin jeji kuma a lokacin sanyi.”


Mutanen da suka yi wa annabci, za a jefar da su waje a kan titunan Urushalima, a karkashe su da yunwa da takobi, ba wanda zai binne su, da su, da matansu, da 'ya'yansu mata da maza. Zan sa muguntarsu ta koma kansu.


Zan sa musu masu hallakarwa huɗu, in ji Ubangiji, “da takobi don kisa, da karnuka don yayyagawa, da tsuntsayen sararin sama, da dabbobin duniya don su cinye, su hallakar.


Zan yashe ka, kai da dukan kifayen kogunanka cikin jeji. Za ka fāɗi a fili, ba kuwa wanda zai ɗauke ka, ya binne ka. Zan sa ka zama abincin namomin jeji da tsuntsayen sararin sama.


kamar al'umman da Ubangiji ya hallakar a gabanku. Haka za ku hallaka domin ba ku kasa kunne ga muryar Ubangiji Allahnku ba.”


Gama mutuwa ta shiga tagoginmu, Ta shiga cikin fādodinmu, Ta karkashe yara a tituna, Ta kuma karkashe samari a dandali.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ