Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 6:8 - Littafi Mai Tsarki

8 Ku ji faɗaka, ya ku mutanen Urushalima, Don kada a raba ni da ku, Don kada in maishe ku kufai, Ƙasar da ba mazauna ciki.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Ki ji gargaɗi, ya Urushalima, ko kuwa in juya daga gare ki in mai da ƙasarki kufai don kada wani ya zauna a cikinta.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 6:8
23 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Ko sun goyi 'ya'ya, Zan sa su mutu tun ba su balaga ba. Tasu ta ƙare sa'ad da na rabu da su!”


Ta yi ta karuwancinta a fili, ta bayyana tsiraicinta. Sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita kamar yadda na rabu da 'yar'uwarta.


Amma duk da haka ba su kasa kunne, ko su mai da hankali ba. Amma suka taurare don kada su ji, su karɓi koyarwa.


Na ce, hakika za ka ji tsorona, Ka kuma karɓi horo. Ba za a rushe wurin zamanta ba Bisa ga hukuncin da na yi mata. Amma suka ɗokanta su lalatar da ayyukansu.


Sun juya mini baya, ba su fuskance ni ba, ko da yake na yi ta koya musu, amma ba su saurara ga koyarwata ba.


Kun ƙi in tsauta muku, Kun yi watsi da umarnaina.


Gama na tuba saboda na rabu da kai, Bayan da aka ganar da ni, sai na sunkuyar da kai, Kunya ta kama ni, na gigice, Domin ina ɗauke da wulakancin ƙuruciyata.’


“Ni Ubangiji na ce, zan mai da Urushalima tsibin kufai, Wurin zaman diloli, Zan kuma mai da biranen Yahuza kufai, inda ba kowa.”


Zan sa muryar murna da ta farin ciki, da muryar ango da ta amarya su ƙare a biranen Yahuza da titunan Urushalima, gama ƙasar za ta zama kufai.”


Saboda haka ga abin da Ubangiji Allah ya ce, “Duba, zan kwarara fushina da hasalata a kan wannan wuri, a kan mutum duk da dabba, da akan itatuwan saura da amfanin gona. Zai yi ta cin wuta, ba kuwa za a kashe ba.”


Ya Urushalima, ki wanke mugunta daga zuciyarki, Domin a cece ki, Har yaushe mugayen tunaninki za su yi ta zama a cikinki?


Zakuna suna ruri a kansa, Suna ruri da babbar murya. Sun lalatar da ƙasarsa, Garuruwansa sun lalace, Ba wanda yake zaune cikinsu.


Kullum ka tuna da abin da ka koya, iliminka shi ne ranka, ka lura da shi da kyau.


Ya Ubangiji, mai farin ciki ne mutumin da kake koya wa, Mutumin da kake koya masa shari'arka.


Yanzu ku kasa kunne gare ni, ku sarakuna, Ku mai da hankali, ku mahukunta!


Da suna da hikima, da sun gane wannan, Da za su gane da yadda ƙarshensu zai zama!


Sa'an nan ƙasar za ta ji daɗin hutunta muddin tana zaune kango. Sa'ad da kuke a ƙasar maƙiyanku, ƙasar za ta huta, taji daɗin hutunta.


Za ka faɗa musu ka ce, wannan ita ce al'ummar da ba ta yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnta ba, ba ta karɓi horo ba. Gaskiya kuma ta ƙare sam, ba ta a bakinsu.


Ka saurari shawara, ka yarda ka koya, wata rana za ka zama mai hikima.


Gama uwarsu ta yi karuwanci. Ita wadda ta haife su ta yi abin kunya. Gama ta ce, ‘Zan bi samarina Waɗanda suke ba ni ci da sha, Da ulu, da lilin, da mai, da ruwan inabi.’


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ