Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 6:25 - Littafi Mai Tsarki

25 Kada ku fita zuwa gona, Kada kuma ku yi yawo a kan hanya, Gama abokin gāba yana da takobi, Razana a kowane sashi.”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

25 Kada ku fita zuwa gonaki ko ku yi tafiya a hanyoyi, gama abokin gāba yana da takobi, kuma akwai razana ko’ina.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 6:25
20 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Za a kwashe alfarwansu da garkunansu, Da labulan alfarwansu, da dukan kayansu. Za a kuma tafi da raƙumansu, Za a gaya musu cewa, ‘Razana ta kewaye ku!’


Na ji mutane da yawa suna sa mini laƙabi cewa, ‘Razana ta kowace fuska,’ Suna cewa, ‘Mu la'anta shi! Mu la'anta shi!’ Har ma da abokaina shaƙiƙai Suna jira su ga fāɗuwata. Suka ce, ‘Watakila a ruɗe shi, Sa'an nan ma iya rinjayarsa Mu ɗauki fansa a kansa.’


Idan na tafi cikin saura, Sai in ga waɗanda aka kashe da takobi! Idan kuma na shiga birni, Sai in ga waɗanda suke ta fama da yunwa! Gama annabi da firist, sai harkarsu suke ta yi a ƙasar, Amma ba su san abin da suke yi ba.’ ”


Na ji magabtana da yawa suna raɗa, Razana ta kewaye ni! Suna ƙulla maƙarƙashiya don su kashe ni.


“Kewaye da shi duka razana tana jiransa, Duk inda ya nufa tana biye da shi,


Don lokaci zai auko muku da maƙiyanku za su yi muku ƙawanya, su yi muku zobe, su kuma tsattsare ku ta kowane gefe,


Mutanen Urushalima sun ce, “Don me muke zaune kawai? Bari mu tattaru, mu tafi cikin garuruwa masu garu, Mu mutu a can, Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa, Ya ba mu ruwan dafi, Domin mun yi masa laifi.


Sai na ce, “Kaito, kaito, ya Ubangiji Allah, ka ruɗi jama'an nan da Urushalima, da ka ce musu, ‘Za ku zauna lafiya,’ amma ga shi, takobi zai sassare su.”


“Ku yi shela a cikin Yahuza, Ku ta da murya a Urushalima, ku ce, ‘Ku busa ƙaho a dukan ƙasar!’ Ku ta da murya da ƙarfi, ku ce, ‘Ku tattaru, mu shiga birane masu garu.’


Amma idan kuka ƙi, kuka raina ni, mutuwa ce ƙaddararku. Ni Ubangiji na faɗi wannan.”


A waɗancan lokatai, ba salama ga mai fita ko ga mai shiga, gama babban hargitsi ya wahalar da dukan mazaunan ƙasashe.


“Ni Ubangiji na ce, Mun ji kukan gigitacce, Kukan firgita ba kuma salama.


Ubangiji ya yi tambaya ya ce, “Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, An ci sojojinsu, suna gudu, Ba su waiwayen baya, akwai tsoro a kowane sashi.”


Ka gayyato mini tsoro Kamar yadda akan gayyato taro a ranar idi. A ranar fushin Ubangiji Ba wanda ya tsere, ko wanda ya tsira. 'Ya'yan da na yi renonsu, na goye su, Maƙiyina ya hallaka su.


Mun sa zuciya ga salama, amma ba lafiya, Mun sa zuciya ga lokacin samun warkewa, Amma sai ga razana!


Ga shi, zan kawo muku razana daga waɗanda suke kewaye da ku, Za a kore ku, kowane mutum zai kama gabansa, Ba wanda zai tattara 'yan gudun hijira. Ni Ubangiji Allah Mai Runduna na faɗa.


Sun sa tufafin makoki, razana ta kama su, fuskokinsu kuma suna cike da kunya, akwai sanƙo a kawunansu.


Ni kuma zan tafa hannuwana, zan aukar da fushina, ni Ubangiji na faɗa.”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ