Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 51:34 - Littafi Mai Tsarki

34 Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya cinye Urushalima, Ya ragargaza ta, Ya maishe ta kufai, Ya haɗiye ta kamar yadda dodon ruwa yakan yi, Ya cika cikinsa da kayan marmarinta, Ya tatse ta sarai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

34 “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya cinye mu, ya sa muka rikice, ya maishe mu kamar tulun da babu kome a cikinsa. Ya cinye mu kamar yadda dodon ruwa yakan yi ya kuma cika cikinsa da kayan marmarinmu, sa’an nan kuma ya yi amanmu.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 51:34
21 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

“Isra'ilawa kamar tumaki ne waɗanda zakuna suka bi su suna kora. Da farko dai Sarkin Assuriya ne ya cinye su. Yanzu kuwa Sarkin Babila, wato Nebukadnezzar, shi ne yake gaigayi ƙasusuwansu.


Zan hukunta Bel, gunkin Babila, Zan sa ya yi aman abin da ya haɗiye, Ƙasashen duniya ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Garun Babila ya rushe!”


“Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kun toshe wa mutane ƙofar Mulkin Sama. Ku kanku ba ku shiga ba, kuna kuwa hana masu niyyar shiga shiga.


Mugun mutum yakan harar da dukiyar da ya samu ta hanyar zamba, Allah zai karɓe ta har da wadda ya ci a cikin cikinsa.


Gama Ubangiji zai mayar wa Yakubu da darajarsa kamar ta Isra'ila. Ko da masu washewa sun washe su, Sun kuma lalatar da rassan inabinsu.


Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata, kuna ƙoƙari ku hallakar da matalautan ƙasar.


sai ka yi annabci ka ce, ni Ubangiji Allah na ce, ‘Da yake sun maishe ku kufai marar amfani, sun kuma murƙushe ku ta kowace fuska, har kun zama abin mallakar sauran al'umma, kun zama abin magana da abin tsegumi ga mutane.


Maƙiyanki duka sun wage bakinsu gāba da ke, Suna tsāki, suna cizon bakinsu, Suna ihu, suna cewa, “Mun hallaka ta! Ai, wannan ita ce ranar da muke fata! Ga shi kuwa, ta zo, mun gan ta!”


Urushalima wadda take cike da mutane a dā, Yanzu tana zaman kaɗaici! Tana zama kamar mace wadda mijinta ya rasu, Ita wadda dā ta zama babba a cikin sauran al'ummai! Ita wadda take a dā sarauniya a cikin larduna, Ta zama mai biyan gandu!


Babila za ta fāɗi, Saboda mutanen Isra'ila da dukan mutanen duniya waɗanda ta kashe.


Duk waɗanda suka same su, sun cinye su. Maƙiyansu suka ce, ‘Ba mu yi laifi ba,’ Gama sun yi wa Ubangiji laifi, wanda yake tushen gaskiya, Ubangiji wanda kakanninsu suka dogara gare shi.


Mujiyoyi da hankaki su ne za su gāji ƙasar. Ubangiji zai maishe ta marar amfani, kamar yadda take tun kafin halitta.


Ba mu damu da ransu da lafiyarsu ba, mu dai mu tafi mu kashe su, mu hallaka su ɗungum.


Da ƙarfin ikonka ka raba teku, Ka farfashe kawunan dodannin ruwa,


Isra'ila kamar kowace al'umma ce. Suna cikin al'ummai Kamar kaskon da ba shi da amfani,


Amma yanzu an washe mutanensa, Aka kukkulle su a kurkuku, Aka ɓoye su a rami. Aka yi musu fashi, aka washe su, Ba wanda ya zo domin ya kuɓutar da su.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ