Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 51:1 - Littafi Mai Tsarki

1 Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan kawo iskar ɓarna a kan Babila Da mazaunan Kaldiya.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

1 Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan zuga ruhun mai hallakarwa a kan Babilon da mutanen Leb Kamai.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 51:1
23 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Zai yiwu mutane su rasa firgita, Idan aka busa ƙahon yaƙi a birni? Zai yiwu wata babbar masifa ta auko wa birni Ba da yardar Ubangiji ba?


Ko da yake Isra'ila tana bunƙasa kamar ciyayi, Iskar gabas, wato iskar da za ta zo daga jeji, Za ta busar da maɓuɓɓugarsu da idon ruwansu, Za ta lalatar da abubuwa masu amfani da yake cikin taskarsu.


Sai ya fāɗi, ya kuma ji wata murya tana ce masa, “Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini?”


Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Bayan ɗaukaka ya aike ni zuwa wurin al'umman duniyan nan da suka washe ku, gama wanda ya taɓe ku, ya taɓi ƙwayar idona.


Amma aka tumɓuke kurangar inabin da fushi, Aka jefar da ita ƙasa. Iskar gabas ta busar da ita, 'Ya'yanta suka kakkaɓe, Rassanta masu ƙarfi sun bushe, wuta kuwa ta cinye su.


“Ni Ubangiji Mai Runduna na ce, An danne mutanen Isra'ila da na Yahuza, Duk waɗanda suka kama su bayi sun riƙe su da ƙarfi. Sun ƙi su sake su.


“Ku kirawo 'yan baka, dukan waɗanda sukan ja baka, su faɗa wa Babila. Ku kafa sansani kewaye da ita, kada ku bar kowa ya tsira. Ku sāka mata bisa ga dukan ayyukanta, gama ta raina Ubangiji Mai Tsarki na Isra'ila.


Na kafa miki tarko, ya kuwa kama ki, ya Babila, Ke kuwa ba ki sani ba. An same ki, an kama, Domin kin yi gāba da ni.”


“Ku haura ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da mazaunan Fekod. Ku kashe, ku hallaka su sarai, Ku aikata dukan abin da na umarce ku, Ni Ubangiji na faɗa.


Ga shi, zan kuta manyan ƙasashe daga arewa Su faɗa wa Babila da yaƙi. Za su ja dāgar yaƙi gāba da ita, su cinye ta. Kibansu kamar na gwanayen mayaƙa ne Waɗanda ba su komowa banza.


Zan sa iska ta hura a kan Elam daga kusurwoyi huɗu na samaniya. Za ta watsar da mutane ko'ina, Har ba ƙasar da za a rasa mutumin Elam a ciki.


Ga shi, zan sa wani ruhu a cikinsa da zai ji jita-jita, har ya koma ƙasarsa, zan sa a kashe shi da takobi a ƙasarsa.’ ”


Babila, za a hallaka ki! Mai farin ciki ne shi wanda ya sāka miki Bisa ga abin da kika yi mana.


“Ga shi, hadirin hasalar Ubangiji ya taso, Kamar iskar guguwa, Zai tashi a bisa kan mugaye.


Zan sa sammai su yi rawar jiki, duniya kuwa za a girgiza ta a inda take, a wannan rana sa'ad da ni, Ubangiji Mai Runduna, na nuna fushina.


Kai ka ce za ka hau can bisa kan taurari, ka zama kamar Mai Iko Dukka.


Wannan shi ne jawabi a kan Babila. Kamar yadda guguwa take tasowa daga hamada, haka masifa za ta auko daga wata ƙasa mai razanarwa.


Ubangiji ya ce, “Babila, ki sauko daga kan gadon sarautarki, Ki zauna a ƙasa cikin ƙura. Dā ke budurwa ce, birnin da ba a yi nasara da shi ba! Amma ba sauran taushi da kuma rashin ƙarfi! Ke baiwa ce yanzu!


Ko da Babila za ta hau samaniya, Ta gina kagara mai ƙarfi a can, Duk da haka zan aiki masu hallakarwa a kanta, Ni Ubangiji na faɗa.”


Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babila, wato dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babila.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ