Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 50:34 - Littafi Mai Tsarki

34 Mai fansarsu mai ƙarfi ne, Ubangiji Mai Runduna ne sunansa. Hakika zai tsaya musu don ya kawo wa duniya salama, Amma zai kawo wa mazaunan Babila fitina.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

34 Duk da haka Mai Fansarsu yana da ƙarfi; Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa. Zai kāre muradunsu gabagadi don yă kawo hutu ga ƙasarsu, amma rashin hutu ga waɗanda suke zaune a Babilon.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 50:34
32 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Mahaliccinki zai zama kamar miji a gare ki, Sunansa Ubangiji Mai Runduna! Allah Mai Tsarki na Isra'ila mai fansarki ne, Shi ne mai mulkin dukan duniya!


Ubangiji ya ce, “Zan tsaya muku, Zan ɗaukar muku fansa, Zan sa tekunsu da maɓuɓɓugarsu su ƙafe.


Zan kuɓutar da kai daga hannun mugaye, Zan ɓamɓare ka daga hannun marasa tausayi.”


Allah Mai Tsarki na Isra'ila ya fanshe mu, Sunansa Ubangiji Mai Runduna ne!


Ubangiji ya ce, “Isra'ila, ku kima ne marasa ƙarfi kuma, Kada ku ji tsoro, zan taimake ku. Ni Allah Mai Tsarki na Isra'ila, ni ne mai fansarku.


Zan ɗauka fushin Ubangiji ne, Gama na yi masa zunubi, Sai lokacin da ya ji da'awata, Har ya yanke mini shari'a. Zai kawo ni zuwa wurin haske, Zan kuwa ga cetonsa.


Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Ubangiji wanda ya fanshe ku ya ce, “Domin in cece ku zan aiko sojoji gāba da Babila, Zan rushe ƙofofin birni, Sowar mutanen birnin za ta zama kuka.


Ya Allah, ka kuɓutar da ni, Ka kiyaye al'amarina daga marasa tsoronka, Ka cece ni daga ƙaryar mugaye!


Ka yi hamayya da masu hamayya da ni, ya Ubangiji, Ka yi faɗa da masu faɗa da ni!


Ki yi makyarkyata, ki yi nishi, ke Sihiyona, Kamar mace mai naƙuda, Gama yanzu za ki fita daga cikin birni, Ki zauna a karkara, Za ki tafi Babila, daga can za a cece ki. Daga can Ubangiji zai cece ki daga hannun maƙiyanki.


Ubangiji Allahnku ya kāre ku ya ce, “Ina ɗauke ƙoƙon da na ba ku cikin fushina. Ba za ku ƙara shan ruwan inabin da zai sa ku yi tangaɗi ba.


Ubangiji, wanda yake mulkin Isra'ila, ya kuma fanshe su, Ubangiji Mai Runduna, yake faɗar wannan, “Ni ne farko, da ƙarshe, Allah Makaɗaici, Ba wani Allah sai ni.


Ubangiji Mai Iko shi ne kāriyarsu, shi zai yi magana dominsu.


Ubangiji zai yi magana dominsu a kan shari'ar da suke yi, ya nemi ran duk wanda yake neman rayukansu.


Saboda haka, bala'inta zai aukar mata rana ɗaya, Mutuwa, da baƙin ciki, da yunwa. Za a kuma ƙone ta, Domin Ubangiji Allah da yake hukunta ta Mai Ƙarfi ne.”


Amma wanda yake wajen Yakubu ba haka yake ba, Domin shi ne ya halicci dukan abu, Isra'ila kuwa abin mallakarsa ne, Ubangiji Mai Runduna ne sunansa.


Sai ka faɗa wa Isra'ilawa cewa, ‘Ni Ubangiji zan 'yantar da ku daga wulakancin nan da Masarawa suke yi muku. Zan kuɓutar da ku daga bautar Masarawa. Da ƙarfi zan aikata hukuntaina masu iko don in cece ku.


Amma na sani akwai wani a Samaniya Wanda a ƙarshe zai zo ya tsaya mini.


Ubangiji ya amsa ya ce, “Wannan shi ne ainihin abin da zai faru. Za a ƙwace kamammun yaƙi, Za a kuma ƙwace wason da masu baƙin mulki ya yi. Zan yi yaƙi da dukan wanda yake yaƙi da ku, Zan kuwa kuɓutar da 'ya'yanku.


Gama Ubangiji ya fanshi Yakubu. Ya fanshe shi daga hannuwan waɗanda suka fi ƙarfinsa.


Haka Ubangiji ya ce, Shi wanda ya ba da rana ta haskaka yini, Ya sa wata da taurari su ba da haske da dare, Shi ne yakan dama teku, ya sa raƙumanta su yi ruri, Sunansa Ubangiji Mai Runduna.


Kakan nuna madawwamiyar ƙauna ga dubbai, amma kakan hukunta wa 'ya'ya saboda laifin ubanninsu. Ya maigirma Maɗaukaki, Allah, sunanka kuwa Ubangiji Mai Runduna.


“Ka karɓi da'awata, ya Ubangiji, Ka kuwa fanshi raina.


Ubangiji yakan umarci rundunarsa, Rundunarsa mai cika umarninsa babba ce, mai ƙarfi, Gama ranar Ubangiji babba ce mai banrazana. Wa zai iya daurewa da ita?


sai ka ji addu'arsu da roƙe-roƙensu, daga wurin zamanka a Sama, ka sa su yi nasara, ka biya musu muradinsu, ka gafarta wa jama'arka waɗanda suka yi maka zunubi.


Gama shi ba kamar waɗannan yake ba, Shi na Yakubu ne. Shi ne ya yi dukan kome, Kabilan Isra'ilawa gādonsa, Sunansa Ubangiji Mai Runduna.


'Ya'yansu za su zama kamar dā, Jama'arsu kuma za su kahu a gabana, Zan hukunta dukan waɗanda suka zalunce su.


Mai hallaka Mowab da garuruwanta ya taho, Zaɓaɓɓun majiya ƙarfinta sun gangara mayanka, Ni sarki, mai suna Ubangiji Mai Runduna, na faɗa.


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ