Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 5:21 - Littafi Mai Tsarki

21 ‘Ku ji wannan, ya ku wawaye, marasa hankali, Kuna da idanu, amma ba ku gani, Kuna da kunnuwa, amma ba ku ji.’ ”

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

21 Ku ji wannan, ku wawaye marasa azanci, waɗanda suke da idanu amma ba sa gani, waɗanda suke da kunnuwa amma ba sa ji.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 5:21
26 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

“Ɗan mutum, kana zaune a tsakiyar gidan 'yan tawaye da suke da idanun gani, amma ba sa gani, suna da kunnuwa na ji, amma ba sa ji, gama su 'yan tawaye ne.


“ ‘Je ka wurin jama'ar nan, ka ce, Za ku ji kam, amma ba za ku fahimta ba faufau, Za ku gani kuma, amma ba za ku gane ba faufau.


Yadda yake a rubuce cewa, “Allah ya toshe musu basira, Ya ba su ido, ba na gani ba, Da kuma kunne, ba na ji ba, Har ya zuwa yau.”


“Ya makantar da su, ya kuma taurarar da zuciya tasu, Kada su gani da idanunsu, su kuma gane a zuci, Har su juyo gare ni in warkar da su.”


Ubangiji ya ce, “Mutanena wawaye ne, Ba su san ni ba, Yara ne dakikai, Ba su da ganewa. Suna gwanance da aikin mugunta, Amma ba su san yadda za su yi nagarta ba.”


Kuna da idanu, ba kwa gani ne? Kuna da kunnuwa, ba kwa ji ne? Ba kwa kuma tunawa ne?


Ko shamuwa ta sararin sama ma, ta san lokatanta, Tattabara da tsattsewa, da gauraka suna kiyaye lokacin komowarsu. Amma mutanena ba su san dokokina ba.’ ”


Sai na ce, “Waɗannan mutane ba su da kirki, Ba su da hankali, Ba su san hanyar Ubangiji, Ko shari'ar Allahnsu ba.


Irin waɗannan mutane dakikai ne, har ba su san abin da suke yi ba. Sun rufe idanunsu da tunaninsu ga gaskiya.


Ya jama'ata, ƙaƙa kuka zama dakikai, wawaye haka? Sai yaushe za ku koya?


Rassan itatuwa sun bushe sun kakkarye, mata kuwa sun tattara, don su riƙa hura wuta da su. Da yake jama'a ba su gane kome ba, Allah Mahaliccinsu ba zai ji tausayinsu ba, ba zai nuna musu jinƙai ba.


Kashe kuɗi saboda ilimi ba shi da amfanin kome ga wawa, domin ba shi da tunani.


Haka za ku sāka wa Ubangiji, Ya ku wawaye, mutane marasa hikima? Ba shi ne Ubanku, Mahaliccinku ba, Wanda ya yi ku, ya kuma kafa ku?


Duk da haka har wa yau Ubangiji bai ba ku zuciyar ganewa, ko idanun gani, ko kunnuwan ji ba.


Ifraimu kamar kurciya take, marar wayo, marar hankali, Takan tafi Masar da Assuriya neman taimako.


Dukansu dakikai ne wawaye, Koyarwar gumaka ba wani abu ba ne, itace ne kawai!


don gani da ido kam, su gani, amma ba da zuci ba. Ji kuma, su ji, amma ba za su fahimta ba, wai don kada su juyo a yafe musu.”


Gama tun daga halittar duniya al'amuran Allah marasa gănuwa, wato ikonsa madawwami, da allahntakarsa, sun fahimtu sarai, ta hanyar abubuwan da aka halitta kuma ake gane su. Saboda haka mutane sun rasa hanzari.


Allah ya ce, “Kirawo mutanena a ɗakin shari'a. Suna da idanu, amma makafi ne, Suna da kunnuwa, amma kurame ne!


“Ka sanar wa zuriyar Yakubu da wannan, Ka kuma yi shelarsa a Yahuza, ka ce,


Da wa zan yi magana don in faɗakar da shi, don su ji? Ga shi, kunnuwansu a toshe suke, su ji, Ga shi, maganar Ubangiji kuwa ta zama abin ba'a a gare su, Ba su marmarinta.


“Amma suka ƙi ji, suka ba da baya, suka toshe kunnuwansu don kada su ji.


Idanunku sun ga manyan wahalai, da alamu, da mu'ujizai masu girma.


Yanzu kuwa saboda kun aikata waɗannan al'amura, sa'ad da na yi ta yi muku magana, amma ba ku kasa kunne ba, sa'ad da na kira ku, ba ku amsa ba,


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ