Biblia Todo Logo
အွန်လိုင်း သမ္မာကျမ်းစာ

- ကြော်ငြာတွေ -




Irmiya 49:8 - Littafi Mai Tsarki

8 Ku mazaunan Dedan, ku juya, ku gudu, Ku ɓuya cikin zurfafa, Gama zan kawo masifa a kan Isuwa A lokacin da zan hukunta shi,

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ

Sabon Rai Don Kowa 2020

8 Ku juya ku gudu, ku ɓuya a cikin kogwanni masu zurfi, ku da kuke zama a Dedan, gama zan kawo masifa a kan Isuwa a lokacin da zan hukunta shi.

အခန်းကိုကြည့်ပါ။ ကော်ပီ




Irmiya 49:8
22 ပူးပေါင်းရင်းမြစ်များ  

Sojojin ijararta kamar 'yan maruƙa ne, masu yawan kitse, Sun ba da baya, sun gudu, ba su tsaya ba, Domin ranar masifarsu ta zo, Lokacin halakarsu ya yi.


“Ku mazaunan Hazor, ku gudu zuwa nesa, Ku ɓuya cikin zurfafa, ni Ubangiji na faɗa, Gama Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya shirya muku maƙarƙashiya, Ya ƙulla mugun nufi game da ku.


Wannan shi ne jawabi a kan Arabiya. Ya ku jama'ar Dedan, waɗanda ayarorinku suka yi zango a ƙasar Arabiya wadda take faƙo,


Sai sarakunan duniya, da manyan mutane, da sarakunan yaƙi, da ma'arzuta, da ƙarfafa, da kuma kowane bawa da ɗa, suka ɓuya a kogwanni, da kuma a cikin duwatsu,


Ku kashe dukan bijimanta, a kai su mayanka! Kaitonsu, gama kwanansu ya ƙare, Lokacin hukuncinsu ya yi.


“Za a washe raƙumansu da garkunan shanunsu ganima, Zan watsar da masu yin kwaskwas ko'ina, Zan kuma kawo musu masifu daga kowace fuska, Ni Ubangiji na faɗa.


Wanda ya guje wa tsoro, Zai fāɗa a rami, Wanda kuma ya fito daga cikin rami, Tarko zai kama shi. Gama na sa wa Mowab lokacin da zan hukunta ta, Ni Ubangiji na faɗa.


“Ku mazaunan Mowab, ku bar garuruwanku, Ku tafi, ku zauna a kogwanni, Ku zama kamar kurciya wadda take yin sheƙarta a bakin kwazazzabo.


Ku gudu don ku tserar da rayukanku, Ku gudu kamar jakin jeji.


“Ya ku mutanen Biliyaminu, ku gudu neman mafaka, Daga cikin Urushalima! Ku busa ƙaho a Tekowa, Ku ba da alama a Bet-akkerem, Gama masifa da babbar halaka sun fito daga arewa.


Sa'ad da Ubangiji ya zo domin ya girgiza duniya, jama'a za su ɓuya a cikin kogwannin tuddai da ramummukan duwatsu, suna ƙoƙari su ɓuya daga fushinsa, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa.


Sa'ad da Isra'ilawa suka ga sun ƙuntata, gama an matsa su ƙwarai, sai suka ɓuya cikin kogwanni, da cikin ruƙaƙe, da duwatsu, da ramummuka, da kwazazzabai.


Madayanawa kuwa sun fi Isra'ilawa ƙarfi, saboda haka Isra'ilawa suka yi ta ɓuya a kogon dutse, da waɗansu wuraren ɓuya a tsaunuka.


Ubangiji ya shirya takobinsa a can Sama, yanzu kuwa zai buga Edom, wato mutanen can da ya zartar musu da hukuncin hallaka.


domin haka ni Ubangiji Allah zan hukunta Edom. Zan kashe mutanenta da dabbobinta, zan maishe ta kufai. Za a kashe su da takobi, tun daga Teman har zuwa Dedan.


Na ƙi Isuwa da zuriyarsa, na hallaka ƙasarsa ta kan tudu, wurin zamansa kuwa na ba namomin jeji.”


Edomawa, wato zuriyar Isuwa, sun ce, “An rurrushe garuruwanmu, amma za su sāke gina su.” Sa'an nan Ubangiji zai amsa, ya ce, “To, su gina mana, ai, zan sāke rurrushe su. Mutane za su ce da ƙasarsu, ‘Ƙasar mugaye, da al'ummar da Ubangiji yake fushi da ita har abada.’ ”


ကြှနျုပျတို့နောကျလိုကျပါ:

ကြော်ငြာတွေ


ကြော်ငြာတွေ